{"id":63147,"date":"2018-11-20T23:44:16","date_gmt":"2018-11-20T22:44:16","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=63147"},"modified":"2018-11-20T23:44:23","modified_gmt":"2018-11-20T22:44:23","slug":"an-kashe-fiye-da-mutum-40-a-taron-maulidi","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=63147","title":{"rendered":"An kashe fiye da mutum 40 a taron Maulidi"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\">\n<p><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"An injured person is taken to hospital in Kabul\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2018\/11\/An-kashe-fiye-da-mutum-40-a-taron-Maulidi.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p>An kashe akalla mutum 43 a wani harin kunar bakin wake da aka kai a dakin taron da ake gudanar da taron Maulidi a Kabul, babban birnin Afghanistan.<\/figure>\n<p>Jami&#8217;ai sun ce akalla mutum 83 ne suka jikkata lokacin da malaman addinin musulunci suke taro a babban dakin da ke lardin PD15 domin tunawa da zagayowar ranar haihuwar annabi Muhammad (SAW).<\/p>\n<p>Harin shi ne mafi muni da aka kai Kabul a watannin baya bayan nan.<\/p>\n<p>Babu wanda ya dauki nauyin kai harin, sai dai kungiyar IS ta sha daukar alhakin hare-haren da aka kai a birnin a baya bayan nan.<\/p>\n<p>Hare-haren da kungiyar Taliban ke yawan kai wa sun sa an kara tsaurara matakan tsaro.<\/p>\n<ul class=\"story-body__unordered-list\">\n<li class=\"story-body__list-item\">Da gaske ne Shehu Ibrahim Nyass ya bayyana a Maulidin Abuja?<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Hotunan bikin Maulidin Shiekh Ibrahim Nyass a Abuja<\/li>\n<\/ul>\n<p>Akalla mutum 1,000 ne a dakin taron lokacin da aka kai harin, in ji jaridar Tolo.<\/p>\n<p>1TV News ta ambato jami&#8217;an kula da lafiya na cewa mutum 24 sun ji mummunan rauni.<\/p>\n<p>Wani manajan da ke kula da dakin taron ya ce dan kunar bakin aken ya tashi bam din da ke jikinsa a tsakiyar masu bikin Maulidin<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\"><\/figure>\n<p>Kungiyar IS ta ce ita ce ta kai hari biyu a Kabul a watan Agusta wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.<\/p>\n<p>Kazalika ita ta kai harin da ya halaka mutane da dama da ke kada kuri&#8217;a lokacin zaben majalisar dokokin kasar a watan Oktoba.<\/p>\n<p>Sai dai a kwanakin baya bayan nan an rika yunkurin sulhu domin kawo karshen irin wadannan hare-hare da aka kwashe shekara da shekaru ana kai wa kasar.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>An kashe akalla mutum 43 a wani harin kunar bakin wake da aka kai a dakin taron da ake gudanar da taron Maulidi a Kabul, babban birnin Afghanistan. Jami&#8217;ai sun ce akalla mutum 83 ne suka jikkata lokacin da malaman addinin musulunci suke taro a babban dakin da ke lardin PD15 domin tunawa da zagayowar [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":63148,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[],"class_list":["post-63147","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/63147","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=63147"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/63147\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/63148"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=63147"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=63147"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=63147"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}