{"id":511319,"date":"2026-09-18T23:39:24","date_gmt":"2026-09-18T22:39:24","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=511319"},"modified":"2026-09-18T23:44:32","modified_gmt":"2026-09-18T22:44:32","slug":"mutuwar-masu-ha%c6%99ar-maadinaigwamnatin-jihar-niger-ta-sanya-dokar-hana-fita-a-minna","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=511319","title":{"rendered":"Mutuwar Masu Ha\u0199ar Ma\u2019adinai:Gwamnatin jihar Niger ta sanya dokar hana fita a Minna"},"content":{"rendered":"\n<figure class=\"wp-block-image size-large\"><img decoding=\"async\" src=\"file:\/\/\/data\/user\/0\/org.wordpress.android\/cache\/niger-state-governor-umar-bago2828415300432050816.jpg\" alt=\"\" class=\"wp-image-1869\"\/><\/figure>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\"><br><br><br><br>Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya sanya dokar hana fita ta tsawon sa\u2019o\u2019i 12 a Minna\u00a0 babban birnin jihar domin dakile karin tashin hankali da karya doka da oda.<br><br>Gwamnan ya sanar da hakan ne lokacin da ya kar\u0253i bakuncin Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, a ziyarar ta\u2019aziyya da ya kai jihar kan mutuwar wasu mutane 37 a lokacin da su ke tsare a hannun jami&#8217;an hukumar tsaro ta Civil Defence bayan da aka kama su a wurin ha\u0199ar ma&#8217;adanai.<br><br>Gwamnan ya ce dokar hana fitan, wadda ta fara aiki daga yau, za ta kasance daga \u0199arfe 6 na yamma zuwa 6 na safe domin hana hare-hare kan kadarorin gwamnati da na masu kamfanoni masu zaman kansu da masu zanga-zanga ke yi.<br><br>Ya bayyana cewa wa\u0257anda suka mutu suna tsakanin shekaru 14 zuwa 18.<br><br>Ya ce: \u201cBa mu san ainihin dalilin ba tukuna amma akwai yiwuwar abu biyu. Na farko, daga rahoton da muka samu, an kama mutane 67 aka tsare su a ofishin Civil Defence. Wasu daga cikin wa\u0257anda suka tsira sun ce rashin iska da \u0199ishirwa ne ya kashe su. A zahiri, binciken asibiti da dakin ajiye gawa ya nuna cewa wasu daga cikin gawarwakin suna da kumfa a baki tare da jini da kuma fatar jiki tana \u0253arewa . Saboda haka ba za mu iya kawar da yiwuwar guba ba.\u201d<br><br>Ya kara da cewa: \u201cAn dakatar da kwamandan jihar wanda ya bayar da umarnin tsare mutanen fiye da sa\u2019o\u2019i 24 a cikin \u0257aki \u0257aya. Wannan rashin tausayi ne. Jami\u2019an da ke bakin aiki sun ce sun ji ihun mutanen suna neman taimako amma suka yi kunnen uwar shegu.\u201d<br><br>Bago ya ce an lalata motocin kamfanin sufuri na jihar da ofisoshin jam\u2019iyyar APC su, yana mai cewa \u201c\u2019yan ta\u2019adda sun mamaye tituna, dole ne mu dakile hakan domin samun zaman lafiya.\u201d<br><br>Ya kuma sanar da haramta dukkan ayyukan hakar ma\u2019adinai a jihar tare da umartar ma\u2019aikatan su daina zuwa wuraren aiki.<br><br>Gwamnan ya roki jama\u2019a da su yi hakuri tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta binciko ainihin dalilin faruwar lamarin domin kauce wa faruwar haka anan gaba.<br><br>Ya ce ayyukan hakar ma\u2019adinai ba bisa ka\u2019ida ba suna jawo yara su bar makaranta.<br><br>Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, wanda ya zo tare da Babban Kwamandan NSCDC, ya bayyana lamarin a matsayin abin bakin ciki.<br><br>Ya ce shugaban \u0199asa yana cikin damuwa kan lamarin, kuma zai iya shafar ci gaban gwamnati a matakin jiha da na tarayya.<br><br>Tunji-Ojo ya tabbatar da cewa ba za a sake samun irin wannan lamarin ba, tare da alkawarin cewa za a tabbatar da adalci.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya sanya dokar hana fita ta tsawon sa\u2019o\u2019i 12 a Minna\u00a0 babban birnin jihar domin dakile karin tashin hankali da karya doka da oda. Gwamnan ya sanar da hakan ne lokacin da ya kar\u0253i bakuncin Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, a ziyarar ta\u2019aziyya da ya kai jihar kan [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":2,"featured_media":511232,"comment_status":"closed","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[19017],"class_list":["post-511319","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-niger-maadanai"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511319","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/2"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=511319"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511319\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":511320,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511319\/revisions\/511320"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/511232"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=511319"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=511319"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=511319"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}