{"id":511285,"date":"2026-09-17T05:45:38","date_gmt":"2026-09-17T04:45:38","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=511285"},"modified":"2026-09-17T05:46:13","modified_gmt":"2026-09-17T04:46:13","slug":"dakarun-najeriya-sun-ku%c9%93utar-da-mutane-31-daga-hannun-yan-bindiga-a-katsina-da-kebbi","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=511285","title":{"rendered":"Dakarun Najeriya Sun Ku\u0253utar Da Mutane 31 Daga Hannun \u2019Yan Bindiga A Katsina Da Kebbi"},"content":{"rendered":"\n<p class=\"wp-block-paragraph\"><br><br>Dakarun Rundunar Fansan Yamma da ke gudanar da ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya sun ce sun ku\u0253utar da mutane 31 da \u2019yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihohin Katsina da Kebbi.<br><br>Rundunar ta kuma ce dakarunta sun kama wasu mutane biyu da ake zargi \u2019yan ta\u2019adda ne, tare da \u0199wato alburusai, wasu kayan aikin kai hari, babur da kayan sarki.<br><br>A wata sanarwa da jami\u2019in ya\u0257a labarai na rundunar, Laftanar Kanar Aliyu \u018aanja, ya fitar, ya ce dakarun ha\u0257in gwiwar sun gudanar da ayyukan tsaro a jihohin biyu a ranakun Litinin da Talata.<br><br>A Katsina, dakarun sun ku\u0253utar da mutane 10, da suka ha\u0257a da maza uku da mata bakwai, bayan samun kiran neman agaji kan sace su a \u0199auyukan Unguwar Daudu da Unguwar Ci-\u0253auna da ke \u0199aramar hukumar Funtuwa.<br><br>A jihar Kebbi kuwa, rundunar ta ce bayan samun sahihan bayanan sirri, dakarunta sun kai samame a \u0199auyukan Fafala da Dadikwa da ke \u0199aramar hukumar Kangiwa.<br><br>Rundunar ta ce musayar wuta tsakanin dakarunta da \u2019yan ta\u2019addan ta tilasta wa \u01b4an bindigar tserewa, lamarin da ya ba dakarun damar ku\u0253utar da wasu mutane 21.<br><br>Haka kuma, dakarun sun kama wasu mutane biyu da ake zargi da ta\u2019addanci a yankin \u01b3antumaki na \u0199aramar hukumar \u018aan Musa a Katsina. A cewar rundunar, binciken farko ya nuna cewa wa\u0257anda ake zargin suna da ala\u0199a da wani \u0257an ta\u2019adda mai suna Mannori.<br><br>Sai dai yayin da rundunar ke bayyana nasarorin, wasu masana harkokin tsaro na ganin akwai bu\u0199atar dakarun Najeriya su \u0199ara matsa lamba kan masu aikata laifuka tare da kai ayyukan sintiri da farmaki cikin dazuzzukan da ake zargin \u2019yan bindiga na fakewa, domin dakile ayyukansu.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Dakarun Rundunar Fansan Yamma da ke gudanar da ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya sun ce sun ku\u0253utar da mutane 31 da \u2019yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihohin Katsina da Kebbi. Rundunar ta kuma ce dakarunta sun kama wasu mutane biyu da ake zargi \u2019yan ta\u2019adda ne, tare da \u0199wato [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":6,"featured_media":511284,"comment_status":"closed","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[443,4047,271],"class_list":["post-511285","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-kebbi","tag-najeriya","tag-zamfara"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511285","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/6"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=511285"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511285\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":511286,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511285\/revisions\/511286"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/511284"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=511285"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=511285"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=511285"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}