{"id":511103,"date":"2026-09-02T22:49:20","date_gmt":"2026-09-02T21:49:20","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=511103"},"modified":"2026-09-02T22:49:53","modified_gmt":"2026-09-02T21:49:53","slug":"rikici-ya-lalata-makarantu-1400-ya-kashe-malamai-2295-a-arewa-maso-gabas","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=511103","title":{"rendered":"Rikici Ya Lalata Makarantu 1,400, Ya Kashe Malamai 2,295 A Arewa Maso Gabas"},"content":{"rendered":"\n<p class=\"wp-block-paragraph\"><br><br>Gwamnatin Jihar Borno ta bayyana cewa sama da makarantu 1,400 sun lalace a yankin Arewa maso Gabas sakamakon shekaru na rikice-rikicen tsaro, yayin da aka kashe malamai 2,295 tare da raba wasu 19,000 da muhallansu.<br><br>Mataimakin Gwamnan Borno, Umar Usman Kadafur, ne ya bayyana hakan a Maiduguri yayin taron kasa na kwanaki biyu kan tasirin rikice-rikice ga tunanin yara a Najeriya.<br><br>Kadafur ya ce kusan yara miliyan uku na bukatar tallafin ilimi na gaggawa, yayin da illar rikicin ke ci gaba da shafar tunaninsu, dabi&#8217;unsu da makomarsu.<br><br>Ya ce, \u201cRaunin tunani ba ya kare idan bindigogi suka yi shiru. Yana shiga cikin kwakwalwarsu da ke ci gaba da bunkasa. Yana sauya fahimtarsu, dabi&#8217;unsu da kuma damar da suke da ita ta amincewa da mutane.\u201d<br><br>Mataimakin gwamnan ya yi gargadin cewa rashin kula da matsalolin tunanin yaran da rikici ya shafa na iya jefa su cikin kiyayya, warewa daga al&#8217;umma da kuma yiwuwar kungiyoyin masu tayar da hankali su dauke su.<br><br>Ya bukaci gwamnati ta samar da tsarin kasa na kula da lafiyar kwakwalwar yaran da rikici ya shafa, tare da kara tura kwararru zuwa yankunan da matsalar ta fi kamari.<br><br>Daraktan Medical Intelligence, Dr Patience Omokri, wadda ta wakilci Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, ta ce ya kamata a dauki raunin tunanin yara a matsayin batun tsaron kasa.<br><br>A cikin sakon Ribadu, ya ce, \u201cYaron da ya samu rauni a tunaninsa ba wanda aka zalunta kawai ba ne. Idan ba a tallafa masa ba, zai iya zama tushen rashin zaman lafiya.\u201d<br><br>UNICEF ta ce yara 270,864 a jihohin Borno, Adamawa da Yobe na bukatar tallafin lafiyar kwakwalwa da na zamantakewa karkashin shirin bukatun jin kai na shekarar 2026.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Gwamnatin Jihar Borno ta bayyana cewa sama da makarantu 1,400 sun lalace a yankin Arewa maso Gabas sakamakon shekaru na rikice-rikicen tsaro, yayin da aka kashe malamai 2,295 tare da raba wasu 19,000 da muhallansu. Mataimakin Gwamnan Borno, Umar Usman Kadafur, ne ya bayyana hakan a Maiduguri yayin taron kasa na kwanaki biyu kan tasirin [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":6,"featured_media":511102,"comment_status":"closed","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[15146,4047],"class_list":["post-511103","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-arewa-maso-gabas","tag-najeriya"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511103","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/6"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=511103"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511103\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":511104,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/511103\/revisions\/511104"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/511102"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=511103"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=511103"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=511103"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}