{"id":508085,"date":"2026-01-27T04:23:56","date_gmt":"2026-01-27T03:23:56","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=508085"},"modified":"2026-01-27T04:24:23","modified_gmt":"2026-01-27T03:24:23","slug":"hukumomin-tsaro-sun-samu-jamian-soji-16-da-laifin-yunkurin-juyin-mulki","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=508085","title":{"rendered":"Hukumomin Tsaro Sun Samu Jami\u2019an Soji 16 Da Laifin Yunkurin Juyin Mulki"},"content":{"rendered":"\n<p class=\"wp-block-paragraph\"><\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Hukumomin tsaron Najeriya sun bayyana cewa sun samu wasu jami\u2019an soji da laifin yunkurin kifar da gwamnati a shekarar da ta gabata.<br><br>Wata sanarwa da shalkwatar tsaron \u0199asa ta fitar ta ce bincike ya tabbatar da laifin wasu \u0199ananan hafsoshi 16, wa\u0257anda ake zargi da shirya yunkurin juyin mulki a watan Oktoban 2025 domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.<br><br>Rundunar sojin \u0199asar ta ce an kama jami\u2019an ne a watan Oktoban bayan zarginsu da rashin ladabi da kuma sa\u0253a wa dokokin aikin soji, lamarin da ya sa aka tsare su tare da bu\u0257e bincike a kansu.<br><br>Sanarwar ta \u0199ara da cewa binciken ya kammala, inda wasu daga cikin sojojin da aka tsare suka amince da shirin yunkurin juyin mulkin, abin da rundunar ta ce ya sa\u0253a wa \u0199a\u2019idojin aikin soji da kuma kundin tsarin mulkin Najeriya.<br><br>Shalkwatar tsaron \u0199asa ta ce nan gaba za a gurfanar da jami\u2019an gaban kotun soji domin yanke musu hukunci.<br><br>A baya-bayan nan, ana yawan jin zarge-zargen yunkurin juyin mulki a Najeriya sakamakon matsalolin tsaro da matsin rayuwa, zarge-zargen da rundunar sojin \u0199asar ta sha musantawa.<br><br>Najeriya ta ta\u0253a fuskantar juyin mulki da dama tun bayan samun \u2019yancin kai, musamman tsakanin shekarun 1966 zuwa 1993. Sai dai tun bayan dawowar mulkin dimokra\u0257iyya a 1999, sojojin \u0199asar ke \u0257aukar duk wani batun yunkurin juyin mulki da matu\u0199ar muhimmanci.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hukumomin tsaron Najeriya sun bayyana cewa sun samu wasu jami\u2019an soji da laifin yunkurin kifar da gwamnati a shekarar da ta gabata. Wata sanarwa da shalkwatar tsaron \u0199asa ta fitar ta ce bincike ya tabbatar da laifin wasu \u0199ananan hafsoshi 16, wa\u0257anda ake zargi da shirya yunkurin juyin mulki a watan Oktoban 2025 domin kifar [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":6,"featured_media":508084,"comment_status":"closed","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[4047,9807],"class_list":["post-508085","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-najeriya","tag-sojoji"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/508085","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/6"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=508085"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/508085\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":508086,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/508085\/revisions\/508086"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/508084"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=508085"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=508085"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=508085"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}