{"id":508015,"date":"2026-01-22T21:35:05","date_gmt":"2026-01-22T20:35:05","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=508015"},"modified":"2026-01-22T21:35:29","modified_gmt":"2026-01-22T20:35:29","slug":"yan-bindiga-sun-kashe-mutane-tara-a-%c9%97an-dume-duk-da-cewa-an-yi-sulhu","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=508015","title":{"rendered":"\u2019Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Tara A \u018aan Dume Duk Da Cewa An Yi Sulhu"},"content":{"rendered":"\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Ana ci gaba da zaman \u0257ar-\u0257ar a garuruwan Kauran Fawa da Unguwar Jika, da wasu yankuna a \u0199aramar hukumar \u018aan Dume ta Jihar Katsina, bayan wani hari da ake zargin \u2019yan bindiga ne suka kai, inda aka kashe mutum tara tare da jikkata wasu 13.<br><br>Harin ya faru ne cikin daren Alhamis, duk da sulhun da masu ruwa da tsaki a yankin suka jagoranta da \u2019yan bindigar, domin dawo da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al\u2019umma.<br><br>Hukumomin yankin sun ce sun halarci jana\u2019izar mutum biyar, yayin da ake ci gaba da \u0257aukar matakai na tabbatar da tsaro a yankin.<br><br>Wani mazaunin \u0257aya daga cikin garuruwan da abin ya shafa, wanda ya bu\u0199aci a sakaya sunansa, ya shaida wa BBC cewa \u2019yan bindigar sun shiga garin ne a \u0199afa suna harbe-harbe.<br><br>&#8220;Mutum tara ne suka mutu sakamakon harbin da yanbindigar suka yi, sannan 13 ne suka samu raunuka inda muka kai su asibiti domin samun kulawa. Sun \u0257auki mutum a\u0199alla goma amma sai suka yi ta sakin mutanen sakamakon artabu. Mutum \u0257aya ne ya rage a hannun su,&#8221; in ji shi.<br><br>Shugaban \u0199aramar hukumar \u018aan Dume, Bishir Hadi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tare da shi aka yi jana\u2019izar mutanen da aka kashe.<br><br>&#8220;Mun yi sulhu kuma mun samu nasara, tsawon wata biyar ba a kawo hari ba sai yanzu. Kafin yanzu babu ranar da ba a kawo mana hari,&#8221; in ji Bishir.<br><br>Jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya ta da\u0257e tana fama da hare-haren \u2019yan bindiga, duk da sulhun da gwamnatin jihar ta yi da su tare da sakin wasu da aka kama, matakin da hukumomi ke cewa an \u0257auke shi ne bisa yarjejeniyar wasu al\u2019ummomi domin samar da zaman lafiya mai \u0257orewa.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Ana ci gaba da zaman \u0257ar-\u0257ar a garuruwan Kauran Fawa da Unguwar Jika, da wasu yankuna a \u0199aramar hukumar \u018aan Dume ta Jihar Katsina, bayan wani hari da ake zargin \u2019yan bindiga ne suka kai, inda aka kashe mutum tara tare da jikkata wasu 13. Harin ya faru ne cikin daren Alhamis, duk da sulhun [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":6,"featured_media":508014,"comment_status":"closed","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[320,4047],"class_list":["post-508015","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-katsina","tag-najeriya"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/508015","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/6"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=508015"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/508015\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":508016,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/508015\/revisions\/508016"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/508014"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=508015"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=508015"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=508015"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}