{"id":491369,"date":"2023-04-06T08:45:47","date_gmt":"2023-04-06T07:45:47","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=491369"},"modified":"2023-04-06T09:22:54","modified_gmt":"2023-04-06T08:22:54","slug":"jinkirin-ci-gaba-da-shariar-ado-doguwa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=491369","title":{"rendered":"Jinkirin ci gaba da shari&#8217;ar Ado Doguwa ba da gangan ba ne &#8211; Gwamnatin Kano"},"content":{"rendered":"\n<figure class=\"wp-block-image size-large is-resized\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/doguwa-819x1024.jpg\" alt=\"\" class=\"wp-image-491391\" width=\"563\" height=\"718\"\/><\/figure>\n\n\n<div id=\"\">\n<div class=\"bbc-1ka88fa ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<figure class=\"bbc-1qdcvv9 e1aczekt0\">\n<div class=\"bbc-172p16q ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-189y18v ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-997y1y eihqrxw0\" style=\"padding-bottom: 56.23931623931624%;\" data-e2e=\"image-placeholder\"><br \/>\n<p>Gwamnatin jihar Kano ta mayar da martani a kan zargin da wasu &#8216;yan fafutuka ke yi cewa ta \u0199i gurfanar da shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai a gaban kotu.<\/p>\n<p>&#8216;Yan sanda sun kama Alhassan Ado Doguwa a \u0199arshen watan Fabarairu, inda suka kai shi kotun majistare bisa zargin ya harbi wasu mutane, kwana \u0257aya bayan za\u0253en shugaban \u0199asa a maza\u0253arsa ta Doguwa\/Tudun wada.<\/p>\n<p>Sun kuma tuhumi \u0257an majalisar wakilan da kashe mutum uku, da raunata wasu takwas a \u0199aramar hukumar Doguwa lokacin da ake kar\u0253ar sakamakon za\u0253e.<\/p>\n<p>Kotun dai, ta ba da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake zargin a gidan yari, kafin fara shari&#8217;a gadan-gadan.<\/p>\n<p>Amma an ga shugaban masu rinjayen a cikin wani bidiyo da ya kara\u0257e shafukan sada zumunta kafin &#8216;yan sanda su kama shi, yana musanta zarge-zargen haddasa tashin hankali a lokacin za\u0253en.<\/p>\n<p>Sai dai, kwana \u0257aya kafin a mayar da shi kotun majistare, sai wata babbar kotun tarayya a Kano ta bayar da belin \u0257an siyasar ranar 6 ga watan Maris.<\/p>\n<p>Tun daga lokacin kuma ba a sake jin batun komawa don ci gaba da shari&#8217;ar ba. Lamarin dai ya sa \u0253angarori da dama sun fara zargin ko hukumomi a Kano, na \u0199o\u0199arin danne maganar, har ta bi ruwa.<\/p>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">To amma a martanin da ta mayar ranar Laraba, ma\u2019aikatar shari\u2019ar jihar Kano ta ce ba da gangan, ta \u0199i kai shi kotu ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">A cewarta, jinkirin da aka samu wajen ci gaba da shari&#8217;ar, wani al\u2019amari ne, na \u0199o\u0199arin bin tsari don tabbatar da adalci ga kowanne \u0253angare.<\/p>\n<\/div>\n<section class=\"bbc-1n4f7vm ebmt73l0\" dir=\"ltr\" role=\"region\" aria-label=\"Karin bayani\"><\/section>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Kwamishinan shari\u2019a na jihar Kano, Musa Abdullahi Lawan ya ce tun lokacin da aka fara gabatar musu batun Alhassan Ado Doguwa, suka lura cewa akwai kura-kurai.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">&#8221;Don kuwa akwai wasu batutuwa da ba a shigar da su cikin takardun da suka shafi zarge-zargen da ake yi wa \u0257an siyasar ba,&#8221; in ji shi.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">A cewar kwamishinan hakan zai iya kawo cikas a shari\u2019ar, ko da an ci gaba da sauraren ta a kotu.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Gamayyar \u0199ungiyoyin fararen hular jihar Kano ne tun da farko, suka ce mutane da dama, ciki har da wa\u0257anda rikicin na Tudun Wada lokacin zaben ya ritsa da su ne suke korafin cewa har yanzu gwamnati ta \u0199i mayar da wanda ake zargin gaban kotu.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Ibrahim Wayya, shugaban gamayyar ya ce jikin mutanen da abin ya rutsa da su, ya fara yin sanyi saboda ganin take-taken kamar ba za a yi musu adalci ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Sai dai Musa Abdullahi Lawan, kwamishinan shari\u2019a na jihar Kano ya ce \u2018yan \u0199ungiyoyin ba su fahimci ina aka dosa game da zarge-zargen da ake yi wa Alhassan Ado Doguwa ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Abin da ya sa suke ganin kamar wani ne yake \u0199o\u0199arin yin \u0199afar-ungulu, zargin da kuma ba shi da tushe balle makama, a cewarsa.<\/p>\n<\/div>\n<h2 id=\"Ina-aka-kwana-game-da-binciken-yan-sanda\" class=\"bbc-1aaitma eglt09e0\" tabindex=\"-1\">Ina aka kwana game da binciken &#8216;yan sanda?<\/h2>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">An tuntu\u0253i rundunar \u2019yan sandan Kano, don jin inda aka kwana game da binciken da suka ce sun fa\u0257a\u0257a a kan zarge-zargen da ake yi wa \u0257an siyasar, sai dai babu wani \u0199wa\u0199\u0199waran bayani da suka yi wa BBC zuwa yanzu.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Amma kwanan baya, an jiyo babban sufeton &#8216;yan sandan Najeriya yana umartar kwamishinoninsa na jihohi, su gaggauta kammala bincike a kan laifukan za\u0253en da aka samu, don mi\u0199a takardun bayanai ga hukumar za\u0253e da nufin gurfanar da wa\u0257anda ake zargi a gaban kotu nan take.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar 6 ga watan Maris, ta ce &#8216;yan sanda sun kama mutum 203 kan laifuka masu ala\u0199a da za\u0253en shugaban \u0199asa da na &#8216;yan majalisun tarayya, baya ga bindigogi guda 18 a za\u0253en na 25 ga watan Fabrairu.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Sanarwar dai ba ta yi \u0199arin bayani game da ko su wane ne mutanen da &#8216;yan sandan suka kama bisa zargi da aikata laifuka za\u0253en ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Ita dai, hukumar za\u0253en Najeriya ta ce ta yi maraba da matakin rundunar &#8216;yan sandan, na kammala bincike tare da dam\u0199a mata takardun bayanan mutanen.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Ta ce tana zuba ido don kar\u0253ar takardun, kuma cikin hanzari za ta kafa wani kwamiti na ayarin \u0199wararru a fannin shari&#8217;a don bin kadin zarge-zargen da ake yi wa mutanen, da gaske.<\/p>\n<\/div>\n<h2 id=\"Za\u0253en-cike-gi\u0253i-a-DoguwaTudun-wada\" class=\"bbc-1aaitma eglt09e0\" tabindex=\"-1\">Za\u0253en cike gi\u0253i a Doguwa\/Tudun wada<\/h2>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Tashe-tashen hankulan da suka faru a lokacin za\u0253en \u0257an majalisar tarayya na maza\u0253ar da Alhassan Ado Doguwa ke wakilta, sun sanya INEC ta ayyana za\u0253en Doguwa da Tudun Wada a matsayin wanda bai kammala ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Da yake sanar da wannan matakin ranar Laraba 8 ga watan jiya na Maris , jami&#8217;in tattara sakamakon za\u0253e, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce tun da farko, ya yi shelar cewa \u0257an takarar na jam&#8217;iyyar APC ya lashe za\u0253e ne, cikin tursasawa.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Ya ce an soke za\u0253e a tashoshi 13 masu yawan mutanen da za su iya ka\u0257a \u0199uri&#8217;a 6, 917 a maza\u0253ar Doguwa da Tudun Wada.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">Sai dai daga bisani, bayan bita, hukumar za\u0253e ta tabbatar cewa yawan \u0199uri&#8217;un da aka soke, sun zarce tazarar da ke tsakanin manyan &#8216;yan takara biyu a za\u0253en.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr ebmt73l0\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-1y32vyc e17g058b0\" dir=\"ltr\">A ranar Asabar 15 ga wannan wata na Afrilu ne, za a kammala za\u0253en, inda a yanzu, shugaban masu rinjayen yake kan gaba da \u0199uri&#8217;a 39,732 a kan \u0257an takarar da ke rufa masa baya na jam&#8217;iyyar NNPP, da \u0199uri&#8217;a 34,798.<\/p>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/figure>\n<\/div>\n<\/div>","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Gwamnatin jihar Kano ta mayar da martani a kan zargin da wasu &#8216;yan fafutuka ke yi cewa ta \u0199i gurfanar da shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai a gaban kotu. &#8216;Yan sanda sun kama Alhassan Ado Doguwa a \u0199arshen watan Fabarairu, inda suka kai shi kotun majistare bisa zargin ya harbi wasu mutane, kwana \u0257aya [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":491392,"comment_status":"closed","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[17845,30],"class_list":["post-491369","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-ado-doguwa","tag-arewa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/491369","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=491369"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/491369\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/491392"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=491369"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=491369"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=491369"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}