{"id":46343,"date":"2018-09-26T09:01:36","date_gmt":"2018-09-26T08:01:36","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=46343"},"modified":"2018-09-26T09:02:23","modified_gmt":"2018-09-26T08:02:23","slug":"ana-zargin-dogarin-aisha-buhari-da-karbar-biliyoyin-naira","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=46343","title":{"rendered":"Ana zargin dogarin Aisha Buhari da karbar biliyoyin Naira"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\">\n<p><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Uwargidan shugaban Najeriya Aisha Buhari\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2018\/09\/Ana-zargin-dogarin-Aisha-Buhari-da-karbar-biliyoyin-Naira.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Ana zargin babban dogarin uwargidan shugaban Najeriya Aisha Buhari, da laifin karbar kudade daga wasu fitattun mutane a kasar da sunanta.<\/p>\n<p>Uwargidan Shugaban Najeriya Aishatu Buhari ta tabbatar da cewa babban dogarin na hannun jam&#8217;ian tsaron kasar inda yake fuskantar bincike.<\/p>\n<p>Ana dai zargin CSP Sani Baban Inna da kakkarbo kudaden da yawansu ya kai Naira biliyan biyu da rabi daga wasu jami&#8217;an gwamnati da abokan arzikin uwar dakinsa da sunan tallafi zuwa gareta.<\/p>\n<p>Sai dai dangin jami&#8217;in &#8216;yansandan sun musanta wannan zargin.<\/p>\n<p>Tun a ranar jumu&#8217;ar da ta gabata ne dai bayanai suka ce aka kama dogarin na uwar gidan Shugaban kasa Aishatu Buhari a yayin wani samame da &#8216;yan sanda suka kai gidansa bayan da tayi zargin cewa ya zambace ta zunzurutun kudi har Naira miliyan dubu biyu da miliyan dari biyar.<\/p>\n<p>Sai dai kuma in ji bayanan binciken da aka yi a gidan nasa da kuma a asususn ajiyarsa na banki ya nuna babu alamun makudan kudi irin haka a cikinsu.<\/p>\n<p>Amma kuma sakamakon binciken bai kwantawa uwar dakin tasa rai ba ganin cewa &#8216;yan uwansa &#8216;yan sanda suka yi binciken.<\/p>\n<p>Uwargidan shugaban kasa Buhari ta mika maganar ga hannun hukumar &#8216;yan sandan ciki wato SSS wadda ke ci gaba da binciken wannan maganar kawo yanzu.<\/p>\n<p>Sai dai kuma wata sanar wa da ofishinta ya fitar, Hajiya Aisha Buhari ta ce ba ta da hannu a kama shi da kuma tsarewar da aka ci gaba da yi masa.<\/p>\n<p>Sulaiman Haruna shi ne mai magana da yawunta:<\/p>\n<p>&#8220;Kamar yadda kowa ya sani, jami&#8217;in &#8216;yan sanda ne, kuma hukumar &#8216;yan sanda ce da kanta ta kama shi domin ta bincike shi akan wasu zarge-zarge da aka yi masa cewa yaje ya karbi kudade da sunanta, da sunan &#8216;ya&#8217;yanta cewa suna neman kudi.&#8221;<\/p>\n<p>Ya kara da cewa, &#8220;Kuma an sami labarin cewa ya karbi kudade da yawa a hannun mutane.&#8221;<\/p>\n<p>Ko dai mene ne CSP Sani Baban-inna na tsare a halin yanzu yana fuskantar bincike kan wannan zargin da uwargidan shugaban kasar ke yi masa.<\/p>\n<p>Yayin da a bangare guda iyalinsa suka tsaya kai da fata cewa dan uwansu bai aikata laifi makamancin wannan ba.<\/p>\n<p>Ga ta bakin yayansa Faruk Baban-Inna:<\/p>\n<p>&#8220;Dan uwanmu mai gaskiya ne, bai aikata wannan laifin ba, mu a matsayin &#8216;yan uwansa mun tabbatar da haka.&#8221;<\/p>\n<p>Ga alamu &#8216;yan kasar ba su da damuwa ga kamawa da kuma binciken ake yi wa jami&#8217;in dan sandan; wasu na da damuwar ne kan yadda ake ci gaba da tsare shi fiye da sa&#8217;oi 24 ba tare da gurfanar da shi gaban kotu ba.<\/p>\n<p>Wannan dai ba shi ne karon farko da ake kama wani a kasar bisa zargin karbar kudade daga jama&#8217;a da sunan uwargidan shugaban kasar ba.<\/p>\n<p>Ko a watan Janairun bana ma, &#8216;yan sanda a Abuja babban birnin Najeriya sun gurfanar da wata mata mai shekara 37 a gaban kotu bisa zarginta da neman kwangiloli da karbar kudade daga jama&#8217;a da suna cewa ita ce Aisha Buhari.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Ana zargin babban dogarin uwargidan shugaban Najeriya Aisha Buhari, da laifin karbar kudade daga wasu fitattun mutane a kasar da sunanta. Uwargidan Shugaban Najeriya Aishatu Buhari ta tabbatar da cewa babban dogarin na hannun jam&#8217;ian tsaron kasar inda yake fuskantar bincike. Ana dai zargin CSP Sani Baban Inna da kakkarbo kudaden da yawansu ya kai [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":46344,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[1232],"class_list":["post-46343","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-aisha-buhari"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/46343","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=46343"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/46343\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/46344"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=46343"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=46343"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=46343"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}