{"id":453555,"date":"2022-06-27T16:41:11","date_gmt":"2022-06-27T15:41:11","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=453555"},"modified":"2022-06-27T16:41:13","modified_gmt":"2022-06-27T15:41:13","slug":"kyale-kowa-ya-mallaki-makami-a-zamfara-na-da-ha%c9%97ari","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=453555","title":{"rendered":"&#8216;Kyale kowa ya mallaki makami a Zamfara na da ha\u0257ari&#8217;"},"content":{"rendered":"\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Masana a harkar tsaro sun bayyana cewa matakin da gwamnatin jihar Zamfara da ke Najeriya ta dauka na kyale farar-hula su mallaki bindiga yana da matukar hadari.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">A karshen makon jiya ne gwamnatin ta sanar da wannan mataki tana mai cewa ta dauke shi ne&nbsp;<a href=\"https:\/\/www.bbc.com\/hausa\/articles\/cqe28e51g6jo\">sakamakon yawaitar hare-haren &#8216;yan ta&#8217;adda da &#8216;yan fashin daji.<\/a><\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Sai dai wani masani kan harkar tsaro a yammacin nahiyar Afirka, Audu Bulama Bukarti, ya ce shawarar da gwamnatin Zamfara ta yanke za ta iya kawo kazancewar rikici tsakanin Hausawa &#8211; mazauna cikin garuruwa da Fulanin daji &#8211; wadanda ke zargin ana masu rashin adalci.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Ya ce: \u201cYanzu haka Fulani na koke-koken cewa \u2018yan banga na Hausawa sukan je rugage ne su kashe duk Bafulatanin da suka gani, su kona dukiyarsa saboda suna ganin duk Bafulatani yana cikin \u2018yan bindiga.\u201d<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">\u201cHaka kuma Hausawa mazauna cikin gari suna zargin cewa ana kashe su da garkuwa da su ne saboda kabilanci da Fulani suke nuna masu,\u201d a cewarsa.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Ya kara da cewa idan aka ce kowa ya dauki bindiga to kuwa duk Bafulatanin da Hausawa suka gani a daji kashe shi za su yi, haka nan ma duk Bahaushen da Fulani suka gani su ma kashe shi za su yi.<\/p>\n\n\n\n<figure class=\"wp-block-image size-full\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" width=\"800\" height=\"450\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara.webp\" alt=\"\" class=\"wp-image-453557\" srcset=\"https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara.webp 800w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara-600x338.webp 600w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara-768x432.webp 768w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara-150x84.webp 150w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara-300x169.webp 300w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/zamfara-696x392.webp 696w\" sizes=\"(max-width: 800px) 100vw, 800px\" \/><figcaption>Bayanan hoto,&#8217;Yan bindiga sun addabi kauyukan jihar Zamfara<\/figcaption><\/figure>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Saboda haka a cewar Bukarti ya kamata gwamnatin tarayyar Najeriya ta ja kunnen gwamnatin Zamfara kan wannan mataki da ta dauka.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Domin ya ce matakin kyale kowa ya dauki bindiga zai bai wa kowa damar yanke hukunci da kuma daukar doka a kan duk wani da ake zargi, koda kuwa ba ya da laifi.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Gwamnatin ta jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya dai, ta ce ne ta bai wa dukkan &#8216;yan Jihar damar mallakar bindiga domin kare kansu daga &#8216;yan fashin daji da masu garkuwa da mutane.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">A wata sanarwa da Kwamishinan watsa labaran Jihar, Ibrahim Magaji Dosara, ya aike wa manema labarai ranar Asabar, ya ce gwamnati ta dauki matakin ne sakamakon yawaitar hare-haren &#8216;yan ta&#8217;adda da &#8216;yan fashin daji.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">&#8220;Hare-haren ta&#8217;addanci sun kasance abin damuwa ga jama&#8217;a da gwamnatin jiha.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Domin haka ne, don mu magance wannan matsala baki daya a yankunanmu, gwamnati ba ta da zabin da ya wuce daukar matakan da suka hada da bai wa mutane damar shiryawa da kuma mallakar bindigogi domin kare kansu daga &#8216;yan fashin daji,&#8221; in ji sanarwar.<\/p>\n\n\n\n<figure class=\"wp-block-image size-full\"><img decoding=\"async\" width=\"800\" height=\"450\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle.webp\" alt=\"\" class=\"wp-image-453558\" srcset=\"https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle.webp 800w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle-600x338.webp 600w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle-768x432.webp 768w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle-150x84.webp 150w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle-300x169.webp 300w, https:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/matawalle-696x392.webp 696w\" sizes=\"(max-width: 800px) 100vw, 800px\" \/><\/figure>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Gwamnatin ta Jihar Zamfara ta ce ita da kanta za ta shige gaba wajen ganin an saukaka wa mutane hanyar mallakar bindiga, musamman ga &#8220;manoma domin samun makaman da za su kare kansu.&#8221;<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">&#8220;Tuni gwamnati ta kammala shirin raba fom 500 ga masarautu 19 da ke Jihar nan domin bai wa mutanen da ke bukatar mallakar bindigogi domin su kare kansu,&#8221; a cewar sanarwar.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Jihar Zamfara na cikin jihohin da suke fama da matsananciyar matsalar tsaro a Najeriya sakamakon hare-haren &#8216;yan fashin daji da masu garkuwa da mutane.<\/p>\n\n\n\n<p class=\"wp-block-paragraph\">Wadannan hare-hare sun yi sanadin mutuwar daruruwan mutane tare da raba dubbai daga muhallansu.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Masana a harkar tsaro sun bayyana cewa matakin da gwamnatin jihar Zamfara da ke Najeriya ta dauka na kyale farar-hula su mallaki bindiga yana da matukar hadari. A karshen makon jiya ne gwamnatin ta sanar da wannan mataki tana mai cewa ta dauke shi ne&nbsp;sakamakon yawaitar hare-haren &#8216;yan ta&#8217;adda da &#8216;yan fashin daji. Sai dai [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":24,"featured_media":453559,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[17624,2681],"tags":[29,12146,41,13051,271,9542,9343],"class_list":["post-453555","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-securenorth","category-hausa","tag-apc","tag-bello-muhammad-matawalle","tag-buhari","tag-matawalle","tag-zamfara","tag-zamfara-attack","tag-zamfara-killing"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/453555","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/24"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=453555"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/453555\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/453559"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=453555"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=453555"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=453555"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}