{"id":443011,"date":"2022-04-09T05:22:59","date_gmt":"2022-04-09T04:22:59","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=443011"},"modified":"2022-04-09T05:24:06","modified_gmt":"2022-04-09T04:24:06","slug":"za-a-koma-yin-shariar-taaddanci-a-asirce-babbar-kotun-najeriya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=443011","title":{"rendered":"Za a Koma Yin Shari&#8217;ar Ta&#8217;addanci A Asirce \u2013 Babbar Kotun Najeriya"},"content":{"rendered":"<p><img decoding=\"async\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/Za-a-Koma-Yin-Shariar-Taaddanci-A-Asirce-\u2013-Babbar.jpg\"><\/p>\n<div id=\"article-content\">\n<div class=\"wsw\">\n<p>Alkalin babbar kotun tarayya a Najeriya, John Tsoho ya fitar da wata sanarwa mai taken &#8220;sabbin shawarwarin aiki kan sauraron kararrakin ta&#8217;addanci&#8221; da ke bayyana yadda kotun za ta rika gudanar da shari&#8217;un da suka shafi ta&#8217;addanci a gaban kotun.<\/p>\n<p>Ya ce an tsara sabon hukuncin ne domin tabbatar da tsaron dukkan bangarori, daga masu laifin da ma jama\u2019a da kuma tabbatar da adalci.<\/p>\n<p>A gefe guda kuma, jagoran haramtacciyar kungiyar &#8216;yan awaren da ake zargi da laifukan ta&#8217;addanci ya shigar da kara yana zargin cewa ba za a iya yi masa shari&#8217;a ba saboda an tasa keyar sa daga Kenya ba bisa ka&#8217;ida ba, kamar yadda takardun kotu suka nuna.<\/p>\n<p>Nnamdi Kanu shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) ya bace ne daga Najeriya bayan ya tsallake beli a shekarar 2017.<\/p>\n<p>An kama shi bayan shekaru da dama yana gudu. Lauyansa ya ce a shekarar da ta gabata an zalunce shi a tsare a Kenya kafin a mayar da shi Najeriya, lamarin da Babban kwamishinan na Kenya ya musanta.<\/p>\n<p>Lauyan Kanu, Mike Ozekhome, a ranar Alhamis, ya ce ba za a iya yi masa shari\u2019a kan zargin ta\u2019addanci da yada labaran karya da sane ba saboda ba a mika shi ga Najeriya ba bisa wadannan tuhume-tuhumen.<\/p>\n<p>Ozekhome yana rokon kotu da ta bayyana tsare shi a matsayin haramtacciyar doka. Har ila yau karar na neman diyyar naira biliyan 50 (dala miliyan 120) da kuma naira miliyan 100 na kudaden shari\u2019a.<\/p>\n<p>A ranar Juma\u2019a ne ake sa ran wata kotu na daban za ta yanke hukunci kan tuhume-tuhume 15 da ake tuhumar Kanu, wadanda za su iya kawo karshen shari\u2019arsa idan har alkali ya amince da bayannan na lauyansa.<\/p>\n<p>Kanu bai yarda da duk wasu tuhume-tuhumen da ake masa ba.<\/p>\n<p>Kungiyar IPOB, wacce Kanu ya kafa a shekarar 2014, na neman ballewar yankin kabilar Igbo, wadda ta mamaye yankin kudu maso gabashin Najeriya. Hukumomi suna kallon IPOB a matsayin kungiyar ta&#8217;addanci. IPOB ta ce tana son samun &#8216;yancin kai ne ta hanyoyin da ba na tashin hankali ba.<\/p><\/div>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Alkalin babbar kotun tarayya a Najeriya, John Tsoho ya fitar da wata sanarwa mai taken &#8220;sabbin shawarwarin aiki kan sauraron kararrakin ta&#8217;addanci&#8221; da ke bayyana yadda kotun za ta rika gudanar da shari&#8217;un da suka shafi ta&#8217;addanci a gaban kotun. Ya ce an tsara sabon hukuncin ne domin tabbatar da tsaron dukkan bangarori, daga masu [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":443006,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[518],"class_list":["post-443011","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-nnamdi-kanu"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/443011","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=443011"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/443011\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/443006"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=443011"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=443011"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=443011"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}