{"id":429597,"date":"2022-01-03T07:37:06","date_gmt":"2022-01-03T06:37:06","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=429597"},"modified":"2022-01-03T07:37:10","modified_gmt":"2022-01-03T06:37:10","slug":"yan-sanda-sun-kubutar-da-almajiran-da-aka-sace-a-zamfara","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=429597","title":{"rendered":"&#8216;Yan sanda sun kubutar da almajiran da aka sace a Zamfara"},"content":{"rendered":"<div id=\"\">\n<div class=\"bbc-1ka88fa e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<figure class=\"bbc-1qdcvv9 e6bmn90\">\n<div class=\"bbc-172p16q e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-189y18v e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-997y1y e1whu0\" style=\"padding-bottom:56.25%\" data-e2e=\"image-placeholder\">\n<p class=\"bbc-1s1cxbv etq3yw90\" role=\"text\"><span class=\"bbc-1gnhmg2 e1yt7oin0\">Asalin hoton, <\/span><span lang=\"en-GB\">NPF<\/span><\/p>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/figure>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\"><b> Rundunar &#8216;yan sanda a jihar Zamfara ta ce ta dam\u0199a wasu \u0199ananan yara 21 da ta ku\u0253utar, bayan mahaifansu sun tura su zuwa karatun Islamiyya amma &#8216;yan fashin daji suka tare motarsu cikin dare a \u0199arshen mako.<\/b><\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ta ce \u0199ananan yaran sun fito ne daga \u0199aramar hukumar Bakura a kan hanyarsu ta zuwa \u018aan Dume cikin jihar Katsina mai ma\u0199wabtaka, kafin sace su a ranar Juma&#8217;a.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Al\u0199aluma sun nuna cewa an sace \u0257alibai sama da 1000 a cikin shekarar da ta yi bankwana akasari a jihohin Zamfara da Katsina da Kaduna da kuma Neja.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">A cewar jami&#8217;in hulda da jama&#8217;a na rundunar &#8216;yan sanda a jihar Zamfara SP Muhammad Shehu ya fada wa BBC cewa ranar Juma&#8217;a daliban su 19 da mata biyu &#8221; sun kawo daidai dajin Kucheri ne &#8216;yan bindigar suka yi awon gaba da su.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<section aria-label=\"Talla 2\" aria-hidden=\"true\" role=\"region\" data-e2e=\"advertisement\" class=\"e1j2237y7 bbc-113e14a e1e90g5r0\"><\/section>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ya kara da cewa wasu mutane ne suka bulguta ma hadakar jami&#8217;an tsaron yankin wadda ba ta yi wata-wata ba ta tunkari barayin ta kwato su.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">SP Muhammad Shehu ya kuma tabbatar da cewa babu ko da yaro daya daga cikinsu da ya samu rauni ko wata matsala yayin artabun, kuma an kubutar da su duka.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Da BBC ta tambaye shi halin da suke ciki sai ya ce &#8220;suna cikin koshin lafiya domin an duba lafiyarsu babu wani wanda ke cikin wani yanayi na rashin lafiya.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Mun kira jami&#8217;an karamar hukumar mulkin Bakura kuma an hannata musu wadannan yaran don mika su ga iyayensu.&#8221; Inji SP Muhammad Shehu.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Sai dai ya yi gargadin cewa al&#8217;umma su daina tafiyar dare, kasancewar masu satar sun fi ayyuka a lokacin.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Yan awanni kafin sace daliban ranar Juma&#8217;a, maharan sun buda wuta a daidai kauyen na Kucheri, inda suka kashe mace daya suka kuma yi garkuwa da matafiya daga motoci 10.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Wata mata da lamarin ya rutsa da su da harsashi ya raunata wa fuska, ta bayyana wa BBC yadda maharan suka kashe &#8216;yar uwarta.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Mun taso daga garin Jibiya da karfe hu\u0257u na yamma kuma mun isa Funtua da misalin \u0199arfe bakwai da wani abu. Daga nan mun wuto &#8216;Yankara zuwa garin Kuceri. Ba mu san da su ba saboda suna cikin duhu ne. Kawai sai muka ji \u0199arar harbi a ko&#8217;ina,&#8221; in ji ta.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ta kara da cewa direban motar ya ji ana harbinsu, sai ya juya motar zuwa cikin gona, inda ya koma kan titi, amma sai \u0253arayin suka bi su suka harbe tayar motar guda ta baya.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;A lokacin ne wani harsashi da suka harbo ya zoje ni ga kunchi kuma ya wuce ya bi ta cikin kujera, inda ya same ta a kanta.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ta ce saboda harbin, &#8220;gilashin motar ya watse kuma ya shiga cikin ijiyata ya yanke ni.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Daga nan ne direban motar ya wuce da su zuwa garin Wanzamai.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Matar ta ce bayan sun isa Wanzamai sai direban motar ya bukaci jama&#8217;a su ba su agaji, &#8220;Daga nan sai aka zo da wata mota kuma aka saka ni da waccan wadda aka harba a kai domin a kai mu asibiti a &#8216;Yankara&#8221;.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ta kara da cewa, &#8220;Lokacin da muka isa &#8216;Yankara mun \u0257auka harbin da aka yi mata a bayanta ne, sai da muka kai asibiti ne suka duba kuma suka ce a kanta aka harbe ta.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ta bayyana cewa ana cikin kulawa da ita abokiyar tafiyarta ta cika: &#8220;Ana min dressing, kai kafin a gama min dressing ma rai ya yi halinsa.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Matar ta kuma ce ba motar su barayin su ka fara tarewa ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Sun fara tare wata mota kuma suka harbi wani mutum guda a kafa cikin motar, inda shi ma ya juyo kuma ya rinka yi ma direbanmu alama da hannu cewa akwai matsala amma da yake dare ne takwas da rabi shi ya sa bai gani ba.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ta bayyana cewa bayan da direban motar da suke ciki ya juya, shi ma ya rika kokarin sanar da wasu direbobin matsalar da ke wurin amma ba su gane ba.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;To sun dai kama wadannan motocin kuma har sun tafi da mutanen da ke cikin motocin. Sun kama kusan mota goma ciki har da tireloli.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Kauyukan Kucheri da Wanzamai na daga cikin wurare mafiya hadari, inda kusan duka hare-haren baya bayan nan a jihar Zamfara a nan ne suke faruwa.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Kauyukan guda biyu makwabtan juna ne, kuma suna tsakanin garin Tsafe na jihar Zamfara da kuma &#8216;Yankara a jihar Katsina.<\/p>\n<\/div>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Asalin hoton, NPF Rundunar &#8216;yan sanda a jihar Zamfara ta ce ta dam\u0199a wasu \u0199ananan yara 21 da ta ku\u0253utar, bayan mahaifansu sun tura su zuwa karatun Islamiyya amma &#8216;yan fashin daji suka tare motarsu cikin dare a \u0199arshen mako. Ta ce \u0199ananan yaran sun fito ne daga \u0199aramar hukumar Bakura a kan hanyarsu ta [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":429500,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[14515,218],"class_list":["post-429597","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-governor-elrufai","tag-kaduna"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/429597","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=429597"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/429597\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/429500"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=429597"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=429597"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=429597"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}