{"id":396497,"date":"2021-09-23T12:50:49","date_gmt":"2021-09-23T11:50:49","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=396497"},"modified":"2021-09-23T12:51:11","modified_gmt":"2021-09-23T11:51:11","slug":"matasa-sun-kona-gidan-kwamishinan-tsaro-da-na-basarake","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=396497","title":{"rendered":"Matasa Sun Kona Gidan Kwamishinan Tsaro Da Na Basarake"},"content":{"rendered":"<p><img decoding=\"async\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2021\/09\/Matasa-Sun-Kona-Gidan-Kwamishinan-Tsaro-Da-Na-Basarake.jpg\"><\/p>\n<div id=\"article-content\">\n<div class=\"wsw\"><span class=\"dateline\">WASHINGTON DC \u2014 <\/span><\/p>\n<p>Karamar hukumar mulkin ta Isa da ke gabashin jihar Sokoto na daya daga cikin yankunan da suka dade suna fama da matsalar &#8216;yan bindiga, masu kai hare-hare suna kisan jama&#8217;a, satar dabbobi da sace mutane domin karbar kudin fansa.<\/p>\n<p>Lamarin ya kara ta&#8217;azzara a &#8216;yan kwanakin nan, sakamakon kwararowa da &#8216;yan bindigar makwabciyar Zamfara suke yi, biyo bayan luguden wuta da sojin Najeriya suke yi a sansanoninsu.<\/p>\n<p>Wannan yanayin ne ya sa wasu matasa a garin Isa, shelkwatar karamar hukumar mulki ta Isa, suka gudanar da wata zanga-zanga, domin nuna fushinsu.<\/p>\n<p>To sai dai kuma zanga-zangar ta dauki sabon salo, yayin da wani bangare na masu zanga-zangar suka kai farmaki tare da kona gidajen kwamishinan lamurran tsaron jihar, Kanal Garba Moyi mai murabus, da kuma na sarkin Gobir duk a cikin garin na Isa.<\/p>\n<p>Da yake wadanda ke da hannu ga afkawa gidan suna hannun jami&#8217;an tsaro, wakilin Muryar Amurka ya tuntubi wani dan garin kuma shugaban rundunar adalci a jihar Sakkwato, Bashir Altine Guyawa ko me ya ingiza matasan yin hakan, sai ya danganta al&#8217;amarin da matsalar rashin tsaro, kamar yadda ya yi bayani cikin sauti.<\/p>\n<p>A nata haujin rundunar &#8216;yan sandan Najeriya, ta bakin kakakin ta a Sakkwato, ASP Sanusi Abubakar ta tabbatar da aukuwar lamarin .<\/p>\n<p>Wakilin Muryar Amurka ya kuma samu zantawa da sarkin Gobir na Isa Nasiru Ahmad na biyu, wanda aka bubbuge fadar sa, wanda ya bayyana mamakin dalilin kai farmaki a gidansa, duk da kasancewar ba shi ne ke rike da ragamar sha&#8217;anin tsaro ba.<\/p>\n<p>&#8220;A matsayin sarki, babban abin da zan iya yi shi ne ba da shawara, kuma kowa yana ji ina ta rubutawa gwamnati kan matsalolin al&#8217;ummata na sha&#8217;anin tsaro. Bayan wannan ba abin da zan iya yi kuma,&#8221; in ji basaraken na Isa.<\/p>\n<p>Har wayau wakilin Muryar Amurka ya tuntubi kwamishinan tsaron wanda aka Kona gidajensa amma ya ce ba zai maganta ba saboda \u2018yan sanda na binciken batun.<\/p>\n<p>Sai dai wasu majiyoyi da ke da alaka da kwamishinan tsaron, sun ce ana zargin shugaban karamar hukumar mulkin ta Isa, Abubakar Yusuf Dan&#8217;ali da shirya zanga-zangar da kuma kona gidajen kwamishinan.<\/p>\n<p>Masu zargin sun ce shugaban karamar hukumar yana son daukar fansa ne akan tuhumar da ake yi masa na taimakawa &#8216;yan ta&#8217;adda, bayan da aka kama wata mota da ake zargin ta shi ce, da ake amfani da ita waje kai wa &#8216;yan bindiga abinci da makamai a jihar Zamfara.<\/p>\n<p>To sai dai a martanin da ya mayar, shugaban karamar hukumar ya musanta wannan zargin, yana mai cewa shi ma labari kawai ya samu cewa ana zanga-zanga a Isa, alhali yana ma a cikin garin a lokacin.<\/p>\n<p>&#8220;Kawo zargi na, sanadiyyar cewa an kama mota ta tana kai abinci wani wuri ga &#8216;yan ta&#8217;adda, bayan ni ina yaki wadannan &#8216;yan ta&#8217;addar, to wannan ya zama cin mutunci da cin zarafi a gare ni,&#8221; ta bakin Dan&#8217;ali.<\/p>\n<p>Ya kara da cewa wadanda suka shirya zanga-zangar da aka kama su, sun tabbatarwa jami&#8217;an tsaro cewa a kashin kan su ne suka gudanar da ita, illa dai wasu bata-gari ne suka shigo suka sauya al&#8217;amura ba daidai ba.<\/p>\n<p>Masu sharhi akan lamuran yau da kullum dai na ganin sakacin hukumomi ne akan rashin tsaro yasa karamar magana ke zama babba, har jama&#8217;a ke nema wa kansu mafita.<\/p>\n<p>Matsalar rashin tsaro dai a iya cewa ta kure tunanin kowa a Najeriya, sai dai da matakan da ake dauka yanzu a wasu jihohi tare da farmaki da soji ke kaiwa \u2018yan ta&#8217;addar akwai fata na samun saukin matsalolin.<\/p>\n<p><strong><em>(VOA Hausa)<\/em><\/strong><\/div>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>WASHINGTON DC \u2014 Karamar hukumar mulkin ta Isa da ke gabashin jihar Sokoto na daya daga cikin yankunan da suka dade suna fama da matsalar &#8216;yan bindiga, masu kai hare-hare suna kisan jama&#8217;a, satar dabbobi da sace mutane domin karbar kudin fansa. Lamarin ya kara ta&#8217;azzara a &#8216;yan kwanakin nan, sakamakon kwararowa da &#8216;yan bindigar [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":396498,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[1],"tags":[200,9981],"class_list":["post-396497","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-more","tag-sokoto","tag-yan-bindiga"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/396497","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=396497"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/396497\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/396498"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=396497"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=396497"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=396497"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}