{"id":378235,"date":"2021-07-28T07:24:33","date_gmt":"2021-07-28T06:24:33","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=378235"},"modified":"2021-07-28T07:35:41","modified_gmt":"2021-07-28T06:35:41","slug":"me-ya-sa-yan-bindiga-suka-koma-satar-sarakuna-a-najeriya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=378235","title":{"rendered":"Me ya sa &#8216;yan bindiga suka koma satar sarakuna a Najeriya?"},"content":{"rendered":"<div id=\"\">\n<div class=\"bbc-1ka88fa e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<figure class=\"bbc-1qdcvv9 e6bmn90\">\n<div class=\"bbc-172p16q e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-189y18v e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-1k5hvrj e1whu0\" data-e2e=\"image-placeholder\"><img decoding=\"async\" class=\"bbc-fat2bc e1enwo3v0\" alt=\"Sarakuna a Jihar Kaduna\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2021\/07\/Me-ya-sa-yan-bindiga-suka-koma-satar-sarakuna-a.png\" width=\"976\"><\/p>\n<p class=\"bbc-1s1cxbv etq3yw90\" role=\"text\"><span class=\"bbc-1gnhmg2 e1yt7oin0\">Asalin hoton, <\/span><span lang=\"en-GB\">KDSG\/KAJURU EMIRATE<\/span><\/p>\n<\/div>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-3edg7g e57qer20\" dir=\"ltr\"><figcaption dir=\"ltr\" class=\"bbc-adn2ox eede9f50\"><span class=\"bbc-1gnhmg2 e1yt7oin0\">Bayanan hoto, <\/span><br \/>\nSarkin Jaba Danladi Gyet Maude (hagu) da Sarkin Kajuru Alhaji Alhassan Adamu wa\u0257anda &#8216;yan fashin daji suka sace<br \/>\n<\/figcaption><\/div>\n<\/div>\n<\/figure>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\"><b>Satar mutane domin neman ku\u0257in fansa abu ne da ya zama ruwan dare a Najeriya kuma bai tsaya a kan daidaikun mutane da \u0257alibai ba, hatta sarakunan gargajiya ba su tsira ba.<\/b><\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">A cikin mako biyu sarakuna uku aka yi garkuwa da su, kodayake an saki biyu daga cikinsu amma na baya-bayanan har yanzu na hannun &#8216;\u01b4an bindigar.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Sarakunan da suka shiga wannan hali sun ha\u0257a da Sarkin Kajuru Alhaji Alhassan Adamu, wanda aka yi garkuwa da shi tare da iyalan gidansa har da jariri. Duk da cewa daga bisani an sako shi sauran iyalan na hannun masu gatrkuwa da suka nemi kudin fansa har naira miliyan 200.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Kalizaka, a Jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya an yi garkuwa da wani basarake amma daga bisani aka sako shi ba tare da wani karin bayani kan ko an biya kudin fansa ba ko akasin haka.<\/p>\n<\/div>\n<section aria-label=\"Talla 2\" aria-hidden=\"true\" role=\"region\" data-e2e=\"advertisement\" class=\"e1j2237y7 bbc-113e14a e1e90g5r0\"><\/section>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Na baya-bayanan shi ne sarkin Jaba da ke Kaduna, Mr Danladi Gyet Maude, wanda aka sace da yammacin ranar Litinin a jihar Nasarawa yana hanyar tafiya gonarsa.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">\u01b3an sanda sun ce suna iya bakin kokarinsu domin gano inda yake, sai dai bayanan da aka tattara sun nuna cewa &#8216;\u01b4an bindiga a kan babura ne suka yi awon gaba da shi.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Basaraken mai shekara sama da 80 ya kasance mutum na uku cikin sarakunan da aka kai wa hari cikin mako biyu a Najeriya.<\/p>\n<\/div>\n<h2 class=\"bbc-1v2sszr e14hemmw0\" id=\"Neman-ku\u0257in-fansa-mai-gwa\u0253i\" tabindex=\"-1\">&#8216;Neman ku\u0257in fansa mai gwa\u0253i&#8217;<\/h2>\n<div class=\"bbc-1ka88fa e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<figure class=\"bbc-1qdcvv9 e6bmn90\">\n<div class=\"bbc-172p16q e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-189y18v e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-1k5hvrj e1whu0\" data-e2e=\"image-placeholder\"><\/div>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/figure>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">A matsayinsu na ma&#8217;adanan al&#8217;adun al&#8217;umma, ana matukar girmama sarakuna a cikin al&#8217;umma. Kuma har yanzu babu wani sahihin bayanai kan abin da ya sa &#8216;\u01b4an bindiga suka koma kai musu farmaki.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Sai dai masu sharhi irinsu Dokta Muhammad Kabir Isa na cewa &#8216;\u01b4an bindiga a galibin lokuta suna far wa irin wa\u0257anan mutane ne bayan sun yi bincike da fahimtar cewa za su samu ku\u0257in fansa mai gwa\u0253i.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ya ce sarakunan da suke far wa masu daraja ta \u0257aya ne da suke ganin suna da ku\u0257i mai yawa, kuma idan za a lura, &#8220;sarakunan na kauyuka ake \u0257auka domin sun lura cewa \u0257aukar \u0199auyawa [talakawa] ba zai biya bukatunsu ba&#8221;.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Sace irin wa\u0257annan mutane na \u0199ara musu yawan kudin fasa da za su karba. Kuma a galibin lokuta da \u0257an gari akan ci gari. Akwai ha\u0257in bakin makusanta sarakuna wajen kai musu hari ko sace su&#8221;, in ji Dokta Muhammad.<\/p>\n<\/div>\n<h2 class=\"bbc-1v2sszr e14hemmw0\" id=\"Babu-wanda-ya-tsira\" tabindex=\"-1\">&#8216;Babu wanda ya tsira&#8217;<\/h2>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Masanin ya ce lura da yadda garkuwa da sarakuna ke sake girmama, &#8220;wannan na nuna cewa tsaro a Najeriya ya gama ta\u0253ar\u0253arewa domin a wannan yanayi da ake ciki babu wanda ya tsira&#8221;.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ya nuna takaicinsa kan rashin isassun jami&#8217;an tsaro da kayan aikin zamani wanda yake cewa shi ke taka rawa a dimbin matsalolin da ake gani.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Babu kayan aikin zamani, babu horo kamar yayda ake gani a ketare, ga rashawa, don haka matsalolin tsaro ba wanda nan kusa za a ga saukinsu ba ne.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<h2 class=\"bbc-1v2sszr e14hemmw0\" id=\"Amfani-da-kimiyya-da-fasaha\" tabindex=\"-1\">Amfani da kimiyya da fasaha<\/h2>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Dokta Muhammad ya ce masu bindigar nan sun wuce tunani domin ba wai kasafai suke kai hari ba, su ma suna amfani da hanyoyin zamani wajen ayyukansu.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ya ce: &#8220;Baya ga makamai, alamomi na nuna cewa suna nazarin abubuwa da ke faruwa da amfani da jirage marasa matuka wajen satar bayanai kan abubuwa da ke faruwa kafin kai hari.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Saboda haka sun fi karfin mahukunta da irin matakan da hukumomi ke dauka a yanzu, dole sai an tashi tsaye an ha\u0257a-kai wajen yakar su.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">&#8220;Sannan su kansu Fulani da ke daji dole sai sun taimaka wa hukumomi wajen yakar &#8216;\u01b4an binndigar da ke labewa a dazuka.&#8221;<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-1ka88fa e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<figure class=\"bbc-1qdcvv9 e6bmn90\">\n<div class=\"bbc-172p16q e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-189y18v e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-367mqz e1whu0\" data-e2e=\"image-placeholder\"><\/div>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/figure>\n<\/div>\n<h2 class=\"bbc-1v2sszr e14hemmw0\" id=\"Karin-haske\" tabindex=\"-1\">Karin haske<\/h2>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Ana yi wa sarakuna kallo a matsayin masu taka muhimmiyar rawa wajen samar da masu aikin sa-kai da ke taimakawa wajen samar da tsaro, kamar bai wa mahukunta gudunmawa wajen dakile ayyukan &#8216;yan bindiga masu garkuwa da mutane domin neman kudin fasa a fadin Najeriya.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Sai dai kamar yadda masana tsaro ke cewa far wa sarakunan a wannan lokaci babu shakka abin damuwa ne ga tsaron kasa ganin idan ba su tsira ba ina ga kuma mutanen da suke jagoranta.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Dama tuni mazauna kauyuka suke guduwa birane la&#8217;akari da rashin kwanciyar hankali, zaman zulumi da tunanin harin &#8216;\u01b4an bindiga.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Iyaye da dama sun cire yaransu daga makarantu a kauyuka saboda a kodayaushe sabon labarin garkuwa da dalibai bulla yake yi.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Sama da \u0257alibai 1,000 aka sace domin neman kudin fansa daga Disamban bara zuwa wannan lokaci. Kusan 300 daga cikin wannan adadi da aka sace daga makarantu da ke jihohin Kaduna da Kebbi da Neja har yanzu na hannun &#8216;\u01b4an bindiga.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Gwamnati dai a kullum na cewa tana iya kokarinta wajen murkushe irin wadanan \u0253ata-gari ko &#8216;yan fasjhin daji kamar yadda ake kiran su. Sai dai korafe-korafe da zaman fargaba na karuwa.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-19j92fr e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<p class=\"bbc-ph03xj e1cc2ql70\" dir=\"ltr\">Akwai masu cewa idan sarakuna ba su tsira daga irin wa\u0257anan hare-hare ba da garkuwa da su ina ga mutanen gari &#8211; ko kuma talakawansu kamar yadda ake cewa a fada.<\/p>\n<\/div>\n<div class=\"bbc-1ka88fa e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<figure class=\"bbc-1qdcvv9 e6bmn90\">\n<div class=\"bbc-172p16q e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-189y18v e57qer20\" dir=\"ltr\">\n<div class=\"bbc-367mqz e1whu0\" data-e2e=\"image-placeholder\"><\/div>\n<\/div>\n<\/div>\n<\/figure>\n<\/div>\n<h2 class=\"bbc-1v2sszr e14hemmw0\" id=\"Wasu-labaran-masu-ala\u0199a\" tabindex=\"-1\">(BBC Hausa)<\/h2>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Asalin hoton, KDSG\/KAJURU EMIRATE Bayanan hoto, Sarkin Jaba Danladi Gyet Maude (hagu) da Sarkin Kajuru Alhaji Alhassan Adamu wa\u0257anda &#8216;yan fashin daji suka sace Satar mutane domin neman ku\u0257in fansa abu ne da ya zama ruwan dare a Najeriya kuma bai tsaya a kan daidaikun mutane da \u0257alibai ba, hatta sarakunan gargajiya ba su tsira [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":378258,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[1],"tags":[41,4047,13462],"class_list":["post-378235","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-more","tag-buhari","tag-najeriya","tag-satar-mutane"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/378235","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=378235"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/378235\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/378258"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=378235"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=378235"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=378235"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}