{"id":360014,"date":"2021-06-02T21:47:11","date_gmt":"2021-06-02T20:47:11","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=360014"},"modified":"2021-06-03T11:12:41","modified_gmt":"2021-06-03T10:12:41","slug":"twitter-ya-goge-sakon-buhari-gwamnati-ta-zargi-kamfanin-da-goyon-bayan-fafutukar-ipob-arewa-news","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=360014","title":{"rendered":"Twitter Ya Goge Sakon Buhari, Gwamnati Ta Zargi Kamfanin Da Goyon Bayan Fafutukar IPOB \u2013 AREWA News"},"content":{"rendered":"<div>VOA Hausa<span class=\"dateline\">\u2014 <\/span><br \/>\nKamfanin Twitter ya share wani sashi na kalaman da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi ga masu kokarin ta da husuma a kudu maso gabashin Najeriya.<br \/>\n\u201cDa yawa daga cikin wadanda suke rigima a yau, suna yara kanana ballantana su san irin asarar rayuka da aka yi a lokacin yakin basasa. Mu da muka je filin daga muka kwashe wata 30, mun gani.\u201d<br \/>\nSaboda haka, Buhari ya kara da cewa, \u201cza mu bi su ta yadda suke so.\u201d<br \/>\nBuhari ya furta kalaman ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban hukumar zabe ta INEC, Farfesa Yakubu Mahmood wanda ya gabatar masa a bayanai kan hare-haren da aka rika kai wa ofisoshin hukumar a sassan Najeriya.<br \/>\nAmma ga dukkan alamu, kamfanin na Twitter ya goge rubutun a ranar Laraba, wanda Muryar Amurka ta yi kokarin lalubo shi a shafin na Twitter, amma abin ya ci tura.<br \/>\nAmma kamfanin na Twitter, ya bar wani sako dake cewa, \u201cwannan sakon ya sabawa ka\u2019idojin da Twitter ya shimfida.\u201d<br \/>\nSai dai gwamnatin ta Najeriya, ta bakin ministan yada labarai Lai Mohamed, ta zargi kamfanin na Twitter da nuna goyon baya ga kungiyar IPOB wacce hukumomin Najeriyar suka haramta ta.<br \/>\nRahotanni sun ruwaito Mohamed yana zargin Twitter da yin biris da kalaman da shugaban kungiyar ta IPOB, Nnamdi Kanu yake wallafa a Twitter da shi da magoya bayansa.<br \/>\n\u201cKungiyar da take ba mambobinta umarnin su kai hari kan ofisoshin \u2018yan sanda, su kashe \u2018yan sanda, su kai hari gidan yari, su kashe gandurobobi, sai kuma a ce shugaban kasa ba shi da ikon ya nuna fushinsa? Mohamed ya fadawa manema labarai a Abuja a ranar Laraba, kamar yadda kafafen yada labaran kasar da dama suka ruwaito.<br \/>\nLai ya kara da cewa, \u201cTwitter na da ka\u2019idojinta, amma ta kwan da sanin cewa, ba ka\u2019idoji ba ne na duniya, duk shugaban kasar da ya ga wani abu da bai kwanta masa a rai ba, yana da \u2018yanci ya bayyana ra\u2019ayinsa.\u201d<br \/>\nA \u2018yan watannin baya-bayan nan, yankin kudu maso gabashin Najeriya, na fama da hare-haren \u2018yan bindiga, wadanda ake dangantawa da kungiyar IPOB da ke fafutukar kafa kasar Biafra, ko da yake, ta sha nesanta kanta da rikice-rikicen.<br \/>\nMafi akasarin hare-haren akan kai su ne akan ofisoshin \u2018yan sanda da jami\u2019an tsaro da kuma na hukumar zabe ta INEC.<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>VOA Hausa\u2014 Kamfanin Twitter ya share wani sashi na kalaman da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi ga masu kokarin ta da husuma a kudu maso gabashin Najeriya. \u201cDa yawa daga cikin wadanda suke rigima a yau, suna yara kanana ballantana su san irin asarar rayuka da aka yi a lokacin yakin basasa. Mu da [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":360015,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[41,551,399],"class_list":["post-360014","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-buhari","tag-lai-mohammed","tag-twitter"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/360014","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=360014"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/360014\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/360015"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=360014"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=360014"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=360014"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}