{"id":347617,"date":"2021-05-04T08:30:04","date_gmt":"2021-05-04T07:30:04","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=347617"},"modified":"2021-05-04T08:30:27","modified_gmt":"2021-05-04T07:30:27","slug":"rundunar-sojin-najeriya-ta-nisanta-kanta-daga-karbar-mulkin-kasar","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=347617","title":{"rendered":"Rundunar Sojin Najeriya Ta Nisanta Kanta Daga Karbar Mulkin Kasar"},"content":{"rendered":"<div id=\"article-content\">\n<div class=\"wsw\"><span class=\"dateline\">ABUJA, NIGERIA. \u2014 <\/span><\/p>\n<p>Wani babban lauya a kasar Robert Clarke ne, ya shawarci shugaba Muhammadu Buhari da ya mika mulki na dan lokaci ga rundunar sojin kasar, domin ta samar da maslaha akan dimbin matsalolin tsaro da tattalin arziki da suka yi wa kasar katutu.<\/p>\n<p>A yayin da yake tsokaci a gidan talabijin na CHANNELS, Clarke ya ce sha\u2019anin tabarbarewar tsaro ya kai halin la haula a kasar, ta yadda \u201csoja ne kadai za su iya magance wadannan matsalolin a halin yanzu.\u201d<\/p>\n<p>Clarke, wanda ya ce Najeriya ta kama turbar wargajewa sakamakon rashin tsaro, ya bayyana cewa kamata yayi soji su karbi iko na wuccin gadi, su kuma mayar da kasar bisa tsarin jihohi 6 kamar yadda ta taba zama a can baya.<\/p>\n<div class=\"wsw__embed\">\n<figure class=\"media-image js-media-expand\">\n<div class=\"img-wrap\">\n<div class=\"thumb\"><img decoding=\"async\" alt=\"Babban Lauya Robert Clarke\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2021\/05\/Rundunar-Sojin-Najeriya-Ta-Nisanta-Kanta-Daga-Karbar-Mulkin-Kasar.jpg\"><\/div>\n<\/div><figcaption>\n<span class=\"caption\">Babban Lauya Robert Clarke<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<\/div>\n<p>A cewar babban lauyan, shugaba Buhari na da karfin iko a karkashin kundin tsarin mulki na 1999, da zai mika mulki na dan lokaci ga rundunar soji, tare da dora mata nauyin mayar da kasar a tsarin na jihohi 6 domin daidaita al\u2019amura.<\/p>\n<p>\u201cKasar nan na bukatar dokar ta baci. Kamata yayi shugaba Buhari ya tattauna da \u2018yan majalisun dokoki na tarayya da na jihohi da kuma gwamnoni akan saka dokar nan take,\u201d in ji lauya Clarke.<\/p>\n<p>To sai dai da take maida martani akan wannan batu, rundunar sojin kasar ta ce za ta ci gaba da tsayuwa kaimun kan biyayya ga gwamnati mai ci yanzu, da kuma dukkan tanade-tanaden mulkin dimokaradiyya.<\/p>\n<p>A wata sanarwa daga Daraktan watsa labarai na rundunar tsaro, Janar Onyema Nwachukwu, ta ce rundunar \u201cza ta ci gaba da kauracewa siyasa, goyon bayan gwamnatin farar hula, da kuma da\u2019a da biyayya ga shugaban kasa da kuma kundin tsarin mulkin kasa.\u201d<\/p>\n<div class=\"wsw__embed\">\n<figure class=\"media-image js-media-expand\">\n<div class=\"img-wrap\">\n<div class=\"thumb\"><img decoding=\"async\" alt=\"Shugaban Najeria Muhammadu buhari Tare da manyan hafsoshin tsaro\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2021\/05\/1620112412_78_Rundunar-Sojin-Najeriya-Ta-Nisanta-Kanta-Daga-Karbar-Mulkin-Kasar.jpg\"><\/div>\n<\/div><figcaption>\n<span class=\"caption\">Shugaban Najeria Muhammadu buhari Tare da manyan hafsoshin tsaro<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<\/div>\n<p>Nwachukwu ya kara da cewa sojin kasar za su ci gaba da aiwatar da ayukansu bisa kwarewa, na kare martabar dimokaradiyya da mutuncin kasa, kazalika da kuma tsaron rayuka da dukiyoyin \u2018yan Najeriya.<\/p>\n<p>Don haka sanarwar ta gargadi \u2018yan siyasa da ke ruruta wutar rikicin neman hambarar da gwamnati ta haramtacciyar hanya da su shiga taitayinsu, domin kuwa rundunar sojin a tsaye take wajen kare dimokaradiyya.<\/p>\n<p>Ta kuma tunatar da dukkan jami\u2019an sojin kasar cewa babban laifi ne su ma yi tunanin tsunduma a wannan keta dokar, inda kuma ta sha alwashin hukunta duk wani jami\u2019in soji da ya yarda ya karbi hudubar irin wadannan \u2018yan siyasar.<\/p>\n<div class=\"wsw__embed\">\n<figure class=\"media-image js-media-expand\">\n<div class=\"img-wrap\">\n<div class=\"thumb\"><img decoding=\"async\" alt=\"Buhari Ya Jagoranci Taron Tsaron Kasa Tare Da Manyan Shugabannin Hukumomin Tsaron Najeriya\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2021\/05\/1620112412_769_Rundunar-Sojin-Najeriya-Ta-Nisanta-Kanta-Daga-Karbar-Mulkin-Kasar.jpg\"><\/div>\n<\/div><figcaption>\n<span class=\"caption\">Buhari Ya Jagoranci Taron Tsaron Kasa Tare Da Manyan Shugabannin Hukumomin Tsaron Najeriya<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<\/div>\n<p>Duk da yake sanarwar ta tabbatar da cewa kasar na cikin wani mawuyacin hali, to amma ta ce tana hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro domin samo bakin zaren warware matsalolin, tare da baiwa \u2018yan Najeriya tabbacin cewa \u201cal\u2019amura za su daidaita nan ba da jimawa ba.<\/p>\n<p>A baya-bayan nan dai, Najeriya ta rasa sojoji da dama a yayin da suke aikin tsaron kasa sakamakon hare-haren mayakan Boko Haram a yankunan arewa maso gaba musamman jihohin Borno da Yobe.<\/p>\n<p>Haka ma wani shugaban dakarun sojojin kasar da wasu manyan jami\u2019ai bakwai sun mutu a lokacin da \u2018yan Boko Haram suka kai wani hari a jihar Borno a baya-bayan nan.<\/p>\n<div class=\"wsw__embed\">\n<figure class=\"media-image js-media-expand\">\n<div class=\"img-wrap\">\n<div class=\"thumb\"><img decoding=\"async\" alt=\"Boko Haram ta yi ikirarin kakkabo jirgin saman soji\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2021\/05\/1620112412_438_Rundunar-Sojin-Najeriya-Ta-Nisanta-Kanta-Daga-Karbar-Mulkin-Kasar.jpg\"><\/div>\n<\/div><figcaption>\n<span class=\"caption\">Boko Haram ta yi ikirarin kakkabo jirgin saman soji<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<\/div>\n<p>Najeriya dai na fama da matsalolin tsaro a kusan dukannin yankunan ta kama da mayakan Boko Haram a yankunan arewa maso gabas, \u2018yan bindiga dadi da masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a arewa maso yamma, ayyukan tada zaune tsaye na haramtaccen kungiyar IPOB, mai fafutukar kafa kasar Biyafara, a kudancin kasar, da dai sauran su.<\/p><\/div>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>ABUJA, NIGERIA. \u2014 Wani babban lauya a kasar Robert Clarke ne, ya shawarci shugaba Muhammadu Buhari da ya mika mulki na dan lokaci ga rundunar sojin kasar, domin ta samar da maslaha akan dimbin matsalolin tsaro da tattalin arziki da suka yi wa kasar katutu. A yayin da yake tsokaci a gidan talabijin na CHANNELS, [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":337456,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[5115,41,16639],"class_list":["post-347617","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-army","tag-buhari","tag-i-attahiru-2"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/347617","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=347617"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/347617\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/337456"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=347617"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=347617"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=347617"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}