{"id":267401,"date":"2020-10-08T18:34:16","date_gmt":"2020-10-08T17:34:16","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=267401"},"modified":"2020-10-08T18:35:01","modified_gmt":"2020-10-08T17:35:01","slug":"wasu-matasa-sun-yi-zanga-zangar-bukatar-kawo-karshen-sars-a-abuja","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=267401","title":{"rendered":"Wasu Matasa Sun Yi Zanga zangar Bukatar Kawo Karshen SARS a Abuja"},"content":{"rendered":"<p>VOA Hausa<span class=\"dateline\">\u2014 <\/span><\/p>\n<div id=\"article-content\">\n<div class=\"wsw\">\u2018Yan Najeriya da dama na ci gaba da yin korafe-korafe game da kashe-kashe na ba bu gaira babu dalili da ake zargin rundunar \u2018yan sanda ta musamman masu yaki da manyan laifuffuka wato SARS da yi.<\/p>\n<p>Kiraye-kirayen neman a kawo karshen rundunar \u2018yan sanda ta SARS ya kara kamari ne bayan bullar wani faifan bidiyo da ya nuna jami\u2019an \u2018yan sandan suna jan wasu mazaje biyu a kasa daga hotel har ta kai ga harbe daya daga cikin su a kan titi a jihar Legas, lamarin da ya kai ga sabunta kiran a kawo karshen SARS din gaba daya.<\/p>\n<div class=\"wsw__embed\">\n<figure class=\"media-image js-media-expand\">\n<div class=\"img-wrap\">\n<div class=\"thumb\"><img decoding=\"async\" alt=\"Zanga zangar #ENDSARS Aisha Yesufu\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/10\/Wasu-Matasa-Sun-Yi-Zanga-zangar-Bukatar-Kawo-Karshen-SARS.jpg\"><\/div>\n<\/div><figcaption>\n<span class=\"caption\">Zanga zangar #ENDSARS Aisha Yesufu<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<\/div>\n<p>\u2018Yar fafutuka dake kan gaba-gaba a neman kubutar da \u2018yan matan Sakandaren Chibok da mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da su a watan Afrilun shekarar 2014, Aisha Yesufu, na daga cikin jerin masu zanga-zangar da suka bayyana a shelkwatar \u2018yan sanda a Abuja, ta ce yakamata a dauki matakan da suka dace, domin kashe-kashen ya isa haka.<\/p>\n<p>Jagoran gangamin neman juyin juya hali wato \u201cRevolution Now\u201d kuma mawallafin jaridar yanar gizo ta Sahara reporters, Omoyele Showore, ya mika bukatar a kawo karshen SARS sakamakon kashe-kashen matasa a bisa dalilin irin tufar da suka sanya, wayoyin da su ke rike da su, da kuma neman diyya wa iyalan wadanda ba-su-ji-ba, ba-su-gani-ba da suka rasa ransu a hannun \u2018yan sandan.<\/p>\n<div class=\"wsw__embed\">\n<figure class=\"media-image js-media-expand\">\n<div class=\"img-wrap\">\n<div class=\"thumb\"><img decoding=\"async\" alt=\"Zanga zangar ENDSARS\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/10\/1602171340_672_Wasu-Matasa-Sun-Yi-Zanga-zangar-Bukatar-Kawo-Karshen-SARS.jpg\"><\/div>\n<\/div><figcaption>\n<span class=\"caption\">Zanga zangar ENDSARS<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<\/div>\n<p>Sanata Shehu Sani ya yi jawabi a kan dalilin fitowa zanga-zangar da aka yi, ya ce, SARS bangare ne na rundunar \u2018yan sanda kuma ya kamata ace suna girmama dokar kasa.<\/p>\n<p>Gwamnati dai ta baza jami\u2019an rundunar \u2018yan sanda ta musamman a yaki da manyan laifuffuka a fadin kasar wadanda yawancin lokaci ke aiki babu inifam ko cikakkiyar shiga irin ta jami\u2019an tsaro, sai dai shiga wadda ba a san jami\u2019an tsaro da ita ba.<\/p>\n<p>Jarumai kamar su Falz, Wizkid, Davido sun shiga wannan gangamin neman a kawo karshen SARS inda gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya sha alwashin daukar mataki cikin gaggawa a kan batun.<\/p>\n<p>An kafa rundunar ta SARS a shekarar 1992 domin yaki da karuwar muggan laifuffuka. Saboda wadannan kiraye kiraye babban sufetan \u2018yan sandan kasar ya dakatar da yawancin aikace-aikacen rundunar ta SARS.<\/p>\n<\/div>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>VOA Hausa\u2014 \u2018Yan Najeriya da dama na ci gaba da yin korafe-korafe game da kashe-kashe na ba bu gaira babu dalili da ake zargin rundunar \u2018yan sanda ta musamman masu yaki da manyan laifuffuka wato SARS da yi. Kiraye-kirayen neman a kawo karshen rundunar \u2018yan sanda ta SARS ya kara kamari ne bayan bullar wani [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":267402,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[1],"tags":[15778,28,61],"class_list":["post-267401","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-more","tag-endsars","tag-abuja","tag-police"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/267401","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=267401"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/267401\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/267402"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=267401"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=267401"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=267401"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}