{"id":233847,"date":"2020-07-08T08:28:32","date_gmt":"2020-07-08T07:28:32","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=233847"},"modified":"2020-07-08T08:28:57","modified_gmt":"2020-07-08T07:28:57","slug":"sojojin-burkina-faso-sun-boye-gawarwakin-farar-hula-hrw","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=233847","title":{"rendered":"Sojojin Burkina Faso sun boye gawarwakin farar hula &#8211; HRW"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"BBC\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/07\/Sojojin-Burkina-Faso-sun-boye-gawarwakin-farar-hula-HRW.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nWani sojan Burkina Faso<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\"> Wani rahoto da kungiyar kare hakkin bil&#8217;adama ta Human Rights Watch ta fitar, ya ce an gano gawawwakin mutane dari da tamanin a kaburburan arewacin Burkina Faso inda sojojin gwamnati ke yakar masu tayar da kayar baya.<\/p>\n<p>Kungiyar ta ce akwai hujjojin da suka nuna cewa sojojin ne suka kashe su.<\/p>\n<p>An rika binne mutane ashirin ashirin, a mabanbantan kaburburan da aka hako a kasan gadoji, da filaye da kuma manyan titunan da ke kusa da garin Djibo.<\/p>\n<p>Kungiyar ta bukaci gwamnati ta gano wadanda suka mayar da yankin abin da ta kira &#8216;Dandalin kashe-kashe&#8217;.<\/p>\n<p>Sai dai ministan tsaron Burkina Faso Moumina Cheriff, ya ce kungiyoyin &#8216;yan bindiga da ke sanye da kayan soji wajen kai hare-hare na iya zama abin zargi.<\/p>\n<p><strong>Karanta wasu labaran<\/strong><\/p>\n<p><strong>Karuwar matsalar tsaro a Burkina Faso<\/strong><\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nShugaba Marc Christian Kabor\u00e9<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p><strong>Karuwar matsalar tsaro a Burkina Faso<\/strong><\/p>\n<p>Burkina Faso ta zamo kasa a nahiyar Afrika ta baya bayan nan da ke fuskantar haren haren yan bindiga da ke da nasaba da tsatstsauran ra&#8217;ayin addini daga wasu kungiyoyi.<\/p>\n<p>Masana na ganin cewa hare-haren ta&#8217;addanci na karuwa ne a yammacin Afrika saboda rashin samar da isasshen tsaro daga kasashen.<\/p>\n<p>Gwamnatin kasar na fuskantar matsin lamba a kan ta dauki sabbin matakai na kawar da &#8216;yan ta&#8217;adda.<\/p>\n<p>A watan Janairun 2020 kadai, an kashe mutum a kalla 60 a wasu hare-hare hudu da aka kai a karo daban-daban a arewacin kasar.<\/p>\n<p>Hare-haren masu tayar da kayar bayan wadanda ke da alaka da kungiyar al-Qaeda da IS, sun karu a shekarar da ta wuce, lamarin da ya tursasawa mutane fiye da rabin miliyan barin gidajensu.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Image caption Wani sojan Burkina Faso Wani rahoto da kungiyar kare hakkin bil&#8217;adama ta Human Rights Watch ta fitar, ya ce an gano gawawwakin mutane dari da tamanin a kaburburan arewacin Burkina Faso inda sojojin gwamnati ke yakar masu tayar da kayar baya. Kungiyar ta ce akwai hujjojin da suka nuna cewa sojojin ne suka [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":233848,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[810,5710,10159],"class_list":["post-233847","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-burkina-faso","tag-human-right-activist","tag-troops"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/233847","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=233847"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/233847\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/233848"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=233847"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=233847"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=233847"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}