{"id":233833,"date":"2020-07-08T08:30:06","date_gmt":"2020-07-08T07:30:06","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=233833"},"modified":"2020-07-08T08:31:47","modified_gmt":"2020-07-08T07:31:47","slug":"yan-fashin-daji-sun-sake-auka-wa-%c6%99auyukan-zamfara-da-sokoto","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=233833","title":{"rendered":"&#8216;Yan fashin daji sun sake auka wa \u0199auyukan Zamfara da Sokoto"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Jihar Zamfara\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/07\/Yan-fashin-daji-sun-sake-auka-wa-\u0199auyukan-Zamfara-da-Sokoto.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\n&#8216;Yan fashin daji sun kashe sama da mutum 30 lokacin da suka auka wa kauyen Dan-Gurgu a farkon watan Mayu<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">\u018aumbin mutane ne rahotanni suka ce sun tsere daga gidajensu sakamakon hare-haren &#8216;yan fashin daji a yankunan Isan jihar Sokoto da ma na Zamfara mai ma\u0199wabtaka tun daga farkon wannan mako.<\/p>\n<p>Bayanai daga \u0199aramar hukumar Shinkafi sun ce gomman mutane ne suka fantsama manyan garuruwan yankin kamar ita Shinkafin don ku\u0253uta da rayukansu.<\/p>\n<p>Wata shaida da ta tsere daga \u0199auyen Kamarawa ta fa\u0257a wa BBC daga inda ta fake a cikin daji cewa sun baro gidajensu ne lokacin da suka ga mahara na far wa mazajensu tare da yin awon gaba da dabbobi.<\/p>\n<p>&#8220;A jiya (Litinin) da safe, sai muka ga jiragen sama suna ta yawo a yankinmu, sai suka sauka jejin da \u0253arayin suke, suna ta sako musu bom-bom da bindigogi. Ga sojoji daga sama suna ta yin shuuu,&#8221; in ji matar.<\/p>\n<p>Ta ce sun yi ta murna don kuwa suna tunanin wahala ta yanke musu. &#8220;Muna cewa \u0199ila za a \u0257auke mana mutanen nan ne.&#8221;<\/p>\n<p>Sai dai ta ce lafawar da aka samu ta jami&#8217;an tsaron sai &#8216;yan fashin dajin da suka no\u0199e suka sake far wa \u0199auyukan yankin. Ta ce daren jiya (Litinin) \u0199auye uku suka tayar.<\/p>\n<p>&#8220;Ka ga asibitin Shinkafi, akwai mutane kwakkwance, asibitin Isa, akwai mutane kwakkwance. Yanzu kuma yau (Talata) Kamarawa, tun da mangariba suka shiga, sun gewaye ta gaba \u0257aya,&#8221; in ji shaidar.<\/p>\n<p>Maharan dai sun kai hare-haren ne a kan babura inda suka ri\u0199a harbi kan mai uwa da wabi.<\/p>\n<p>Lamarin na zuwa ne daidai lokacin da mutanen \u0199auyen Danfasa cikin \u0199aramar hukumar Maru a Zamfara ke juyayin sace mata 20 da kuma mutum bakwai da aka kashe a wani hari da yammacin ranar Litinin.<\/p>\n<p>Wani mutumin \u0199auyen ya fa\u0257a yayin zantawa ta wayar tarho cewa suna tsakiyar cin kasuwa a wani \u0199auye mai ma\u0199wabtaka da su ne ranar Litinin lokacin da maharan suka far wa gidajensu a Danfasa da yamma.<\/p>\n<p>A cewarsa, baya ga mutanen da aka jikkata, an kuma kashe mace biyu da namiji biyar cikinsu har da dattijai guda biyu.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Nigerian Army <\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nRundunar sojan Najeriya ta ce ta lalata sansanonin &#8216;yan fashin daji da dama<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Shaidan wanda ya ce an \u0199one kusan rabin \u0199auyensu, ya ce a halin da yake magana ma yana kan hanyarsa ne ta barin yankin saboda rashin tabbas a garuruwansu.<\/p>\n<p>Ya ce daga ciikin mata ashirin da &#8216;yan fashin suka sace har da &#8216;yarsa mai kimanin shekara talatin, ya kuma ce har yanzu ba su ji amo ko labarinsu matan ba.<\/p>\n<p>Mutumin \u0199auyen \u018aanfasa ya kuma koka kan rashin kai musu \u0257auki don ku\u0253utar da iyalinsu da dukiyarsu daga maharan, duk da neman gudunmawar da suka yi a wajen hukumomi.<\/p>\n<p>Jihohin Zamfara da Sokoto da Katsina dai sun da\u0257e suna fama da hare-haren &#8216;yan fashin daji, duk da matakan da gwamnatin Najeriya kan ce tana \u0257auka don kawo \u0199arshensu.<\/p>\n<p>A baya-bayan nan ma sai da Shugaba Muhammadu Buhari ya bai wa al&#8217;ummar jihar Katsina ha\u0199uri tare da cin alwashin \u0257aukar \u0199wa\u0199\u0199waran mataki don mur\u0199ushe &#8216;yan fashin da suka addabi sassan yanki.<\/p>\n<p>Zuwa yanzu dai jami&#8217;an tsaron Najeriya ba su tabbatar ko musanta rahotannin kai wadannan hare-hare ba.<\/p>\n<p>Kuma ga alama sai nan gaba ne za a iya tantance irin \u0253arnar da maharan suka haddasa a \u0199auyukan da suka far wa musamman na baya-bayan nan garin Kamarawa.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Image caption &#8216;Yan fashin daji sun kashe sama da mutum 30 lokacin da suka auka wa kauyen Dan-Gurgu a farkon watan Mayu \u018aumbin mutane ne rahotanni suka ce sun tsere daga gidajensu sakamakon hare-haren &#8216;yan fashin daji a yankunan Isan jihar Sokoto da ma na Zamfara mai ma\u0199wabtaka tun daga [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":233834,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[3773,2681],"tags":[2611,12322,200,271],"class_list":["post-233833","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-crime","category-hausa","tag-bandits","tag-bello-matawalle","tag-sokoto","tag-zamfara"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/233833","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=233833"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/233833\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/233834"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=233833"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=233833"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=233833"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}