{"id":223991,"date":"2020-06-07T08:39:59","date_gmt":"2020-06-07T07:39:59","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=223991"},"modified":"2020-06-07T08:40:31","modified_gmt":"2020-06-07T07:40:31","slug":"coronavirus-a-najeriya-kwana-100-da-%c9%93ullar-cutar","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=223991","title":{"rendered":"Coronavirus a Najeriya: Kwana 100 da \u0253ullar cutar"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"@JIDESANWOOLU\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/06\/Coronavirus-a-Najeriya-Kwana-100-da-\u0253ullar-cutar.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">@JIDESANWOOLU<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Kwana 100 da \u0253ullar cutar korona Najeriya, annobar wadda aka fara gano ta ranar 27 ga watan Fabrairu, a jikin wani baturen \u0199asar Italiya, zuwa yanzu ta harbi mutane kimanin 12,233 a \u0199asar.<\/p>\n<p>Al\u0199aluman da hukumar da\u0199ile cutuka masu ya\u0257uwa ta fitar a daren Asabar sun nuna cewa a cikin kwana 100, korona ta kashe mutum 342 a Najeriya.<\/p>\n<p>Haka zalika annobar ta \u0253ulla a kusan dukkan jihohin \u0199asar, ciki har da babban birnin \u0199asar, in ban da Cross river.<\/p>\n<p>Yawan al\u0199aluman masu cutar da hukumar NCDC ke fitarwa a kullum ya \u0199aru, mai yiwuwa saboda ha\u0253aka gwaje-gwajen da hukumomin \u0199asar suka yi.<\/p>\n<p>Al\u0199aluma na baya-bayan nan da hukumar ke fitarwa na zuwa cikin adadin \u0257aruruwa.<\/p>\n<p>Ko a ranar Asabar 30 ga watan Mayu, hukumar ta ba da rahoton gano mutum 553 da cutar ta sake harba cikin sa&#8217;a 24, ba a dai ta\u0253 samun adadi mai yawan haka ba cikin kwana guda a \u0199asar.<\/p>\n<p>Haka zalika, kusan rabin mutanen da aka gano sun kamu na cikin jihar Legas, inda cutar ta fara \u0253ulla. Yanzu dai al\u0199luman hukuma sun ce akwai masu korona 5,729 a jihar.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">@JIDESANWOOLU<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>Daga ita sai jihar Kano, wadda cutar ta fara bayyana cikinta ranar Asabar 11 ga watan Afrilu. Yawan masu korona a Kano zuwa yanzu ya kusa mutum 1,000.<\/p>\n<p>A baya-bayan nan \u0199wararru sun bayyana damuwa kan \u0199arancin gwajin da ake samu a Kano, suna cewa cutar na da\u0257a fantsama cikin jama&#8217;a kuma ta hanyar gwaji da killace masu cutar ne kawai za a iya shawo kanta.<\/p>\n<p>Gwamnatin Kano dai ta ce za ta \u0199ara \u0199imi ta hanyar bin gida-gida wajen gudanar da aikin gwaji a jihar.<\/p>\n<p>Ranar 23 ga watan Maris ne kusan wata \u0257aya da fara \u0253ullar cutar a Legas, aka ba da rahoton samun mutum na farko da ya fara kamuwa da korona a Abuja.<\/p>\n<p>Tsohon mataimakin shugaban \u0199asar, Atiku Abubakar ya sanar ta hanyar wani sa\u0199on tiwita cewa \u0257ansa, Mohammed Atiku ya kamu har ma an kwantar da shi a asibitin Gwagwalada.<\/p>\n<p>Ko da yake a cikin wani sa\u0199on bidiyo da ya ta\u0253a fitarwa daga inda yake jinya, Mohammed Atiku ya ce tun ranar Juma&#8217;a 20 ga wata, aka tabbatar masa cewa cutar ta harbe shi<\/p>\n<p>Mohammed Atiku dai na daga cikin mutanen da suka fi da\u0257ewa suna jinyar korona a cibiyar killacewa, kafin sallamo shi bayan ya shafe kimanin kwana 40 yana jinya.<\/p>\n<p>Shi da fitattun mutane kamar Gwamna Nasir elrufa&#8217;i na Kaduna da takwaransa na Bauchi, Bala Mohammed da Seyi Makinde na Oyo duk sun yi fama da cutar a tsawon wannan lokaci kuma sun warke.<\/p>\n<p>Haka zalika a tsawon wannan lokaci an samu jihohi irinsu Zamfara da Kebbi, wa\u0257anda suka ce sun sallami duk masu cutar da aka kwantar a cibiyoyin killacewarsu bayan an tabbatar sun warke.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>Sai dai, bayan kimanin mako guda, an sake samun masu cutar biyu a jihar Kebbi.<\/p>\n<p>A ranar Litinin 23 ga watan Maris ne kuma Hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta sanar da samun mutum na farko da ya rasu saboda cutar korona a Najeriya.<\/p>\n<p>Hukumar NCDC ta ce mutumin \u0257an shekara 67 ya dawo Najeriya ne bayan ya je ganin likita Burtaniya, a cewarta mamacin (Injinya Sulaiman A-ci-mugu) ya yi fama da wadansu kwantattun cutuka kafin rasuwarsa.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Facebook<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nEngineer Sulaiman ya yi fama da cutar daji da ciwon suga kafin cutar korona ta kama shi<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>A ranar 7 ga watan Afrilu kuma, Gwamna Masari na jihar Katsina ya sanar cewa Allah Ya yi wa mutum na farko da ya kamu da coronavirus a jiharsa, Dr Aliyu Yakubu rasuwa.<\/p>\n<p>Ya ce likitan wanda ke garin Daura, an ba da rahoton ya yi tafiya zuwa Lagos, kuma bai dade da komawa gida ba, ya kamu da rashin lafiya inda ya kai kansa asibiti kafin cikawarsa.<\/p>\n<p>Cutar korona ta yi sanadin mutuwar Mallam Abba Kyari, shugaban ma&#8217;aikatan fadar shugaban Najeriya ranar Juma&#8217;a 17 ga watan Afrilu<\/p>\n<p>Abba Kyari ya rasu ne a Legas, inda ya koma jinya bayan ya kamu da cutar ranar 24 ga watan Maris..<\/p>\n<p>Bayanan hukumar da\u0199ile cutuka masu ya\u0257uwa na cewa jihar Legas ce ta fi yawan masu korona da suka mutu zuwa yanzu da mutum 67.<\/p>\n<p>Daga ita sai jihar Kano, inda Allah Ya yi wa mutum 48 rasuwa sanadin cutar. Jihar Borno, mutum 26 ne suka mutu, in ji al\u0199aluman NCDC.<\/p>\n<p>A Abuja, mutum 22 ne suka rasu sakamakon cutar zuwa yanzu. Yayin da Katsina kuma aka samu mutuwar masu cutar 20.<\/p>\n<p>Ranar 30 ga watan Maris ne kuma shugaban \u0199asar ya fara \u0257aukar matakin kulle Najeriya, da nufin shawo kan annobar ta korona.<\/p>\n<p>Har yanzu Najeriya ba ta kai ga bu\u0257e harkokin sufurin jiragen samanta ba, haka kuma matakin hana zirga-zirga tsakanin jihohi na ci gaba da aiki.<\/p>\n<p>Duk da yake, an bu\u0257e wuraren ibada a jihohi da dama da kuma babban birnin \u0199asar Abuja, amma har yanzu kasuwanni na ci ne rabi-da-rabi.<\/p>\n<p>Kuma ma, gwamnatin \u0199asar ta ce ba ta sa ranar komawa ci gaba da harkokin koyo da koyarwa a makarantun Najeriya ba.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto @JIDESANWOOLU Kwana 100 da \u0253ullar cutar korona Najeriya, annobar wadda aka fara gano ta ranar 27 ga watan Fabrairu, a jikin wani baturen \u0199asar Italiya, zuwa yanzu ta harbi mutane kimanin 12,233 a \u0199asar. Al\u0199aluman da hukumar da\u0199ile cutuka masu ya\u0257uwa ta fitar a daren Asabar sun nuna cewa a cikin kwana [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":223992,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681,14571],"tags":[14173,397],"class_list":["post-223991","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","category-health","tag-coronavirus","tag-ncdc"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/223991","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=223991"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/223991\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/223992"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=223991"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=223991"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=223991"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}