{"id":220491,"date":"2020-05-24T07:20:07","date_gmt":"2020-05-24T06:20:07","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=220491"},"modified":"2020-05-24T07:21:12","modified_gmt":"2020-05-24T06:21:12","slug":"taliban-ta-tsagaita-wutar-kwana-uku-don-bikin-%c6%99aramar-sallah","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=220491","title":{"rendered":"Taliban ta tsagaita wutar kwana uku don bikin \u0198aramar Sallah"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Afghan troops\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/05\/Taliban-ta-tsagaita-wutar-kwana-uku-don-bikin-\u0198aramar-Sallah.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nAn samu \u0199aruwar kai hare-hare kan dakarun gwamnati a &#8216;yan makwannin nan<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">\u0198ungiyar Taliban ta ba da sanarwar tsagaita wutar kwana uku da gwamnatin Afghanistan wadda za ta fara aiki daga ranar \u0198aramar Sallah a Lahadin nan.<\/p>\n<p>Matakin na zuwa ne bayan \u0199aruwar hare-hare daga \u0199ungiyar &#8216;yan ta-da-\u0199ayar-baya masu tsattsauran ra&#8217;ayi kan dakarun gwamnati cikin makwannin baya-bayan nan.<\/p>\n<p>Shugaba Ashraf Ghani ya yi maraba da sanarwar, kuma ya ce sojojinsa za su mutunta sharu\u0257\u0257an wannan yarjejeniya.<\/p>\n<p>Yarjejeniyar ta tsawon kwana uku mai yiwuwa ne ta ha\u0253\u0253aka fatan raguwar ayyukan tarzoma na tsawon lokaci a \u0199asar.<\/p>\n<p>Sai dai ba a iya tsawaita wata makamanciyar wannan yarjejeniya da aka cimma saboda sallar idi ba a shekara ta 2018.<\/p>\n<p>&#8220;Kada ku kai duk wani hari kan abokan gaba a ko&#8217;ina. Amma idan ma\u0199iya sun auka muku, to ku kare kanku,&#8221; Mai magana da yawun Taliban Zabihullah Mujahid ya bayyana ranar Asabar.<\/p>\n<p>Ya \u0199ara da cewa an ayyana yarjejeniyar ce ta\u0199amaiman don bikin Sallar Idi, wanda ya kawo \u0199arshen watan Ramadan mai tsarki.<\/p>\n<p>&#8220;Ina maraba da wannan sanarwa,&#8221; Shugaba Asharaf Ghani ya wallafa a shafinsa na Tiwita jim ka\u0257an kuma. &#8220;Na umarci [dakarun soji] su yi aiki da yarjejeniyar ta kwana uku amma su kare kansu matu\u0199ar an kai musu farmaki.&#8221;<\/p>\n<p>Al&#8217;ummar Afghanistan da masu sanya na \u0199asashen duniya sun yi fatan ganin an rage tarzoma tsakanin \u0253angarorin biyu sakamakon sanya hannu kan yarjejeniyar janye dakaru da \u0199ungiyar Taliban ta cimma da Amurka a watan Fabrairu.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">AFP<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nJami&#8217;ai ka\u0257an ne a \u0199ungiyar tsaro ta Nato ke jin cewa tsagwaron \u0199arfin soja na iya yin nasara a kan Taliban<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Sai dai an gamu da cikas kan batun ci gaba da \u0199arin tattaunawa game da musayar fursunoni, yayin aka samu \u0199aruwar hare-hare kan dakarun gwamnati cikin &#8216;yan makwannin nan.<\/p>\n<p>Wani hari da aka kai kan wani asbitin haihuwa da ke babban birnin \u0199asar, Kabul a farkon wannan wata ya janyo tofin Allah tsine daga \u0253angarori da dama.<\/p>\n<p>Yayin da Taliban ta musanta hannu a hari, lamarin ya harzu\u0199a Shugaba Ghani har ya ba da umarnin ci gaba da kai hare-hare kan \u0199ungiyar da ma sauran &#8216;yan ta-da\u0199ayar-baya.<\/p>\n<p>Ya zargi masu gwagwarmaya da makamai da bijirewa kiraye-kirayen da aka sha yi don ta\u0199aita ayyukan tarzoma.<\/p>\n<p>A watan jiya, sai da Taliban ta yi watsi da wani kiran gwamnati na a tsagaita wuta a fa\u0257in Afghanistan don martaba watan Ramadan.<\/p>\n<p>Suka ce &#8220;babu hankali&#8221; cikin lamarin maimakon haka suka \u0199ara yawan kai hare-hare kan dakarun gwamnati.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Image caption An samu \u0199aruwar kai hare-hare kan dakarun gwamnati a &#8216;yan makwannin nan \u0198ungiyar Taliban ta ba da sanarwar tsagaita wutar kwana uku da gwamnatin Afghanistan wadda za ta fara aiki daga ranar \u0198aramar Sallah a Lahadin nan. Matakin na zuwa ne bayan \u0199aruwar hare-hare daga \u0199ungiyar &#8216;yan ta-da-\u0199ayar-baya [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":220492,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681,3],"tags":[30,14429,12349,477],"class_list":["post-220491","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","category-news","tag-arewa","tag-ghani","tag-taliban","tag-usa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/220491","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=220491"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/220491\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/220492"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=220491"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=220491"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=220491"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}