{"id":211074,"date":"2020-04-17T22:42:57","date_gmt":"2020-04-17T21:42:57","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=211074"},"modified":"2020-04-17T22:43:32","modified_gmt":"2020-04-17T21:43:32","slug":"bayani-akan-wanda-ya-kamu-da-cutar-korona-a-jihar-jigawa-arewa-news","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=211074","title":{"rendered":"Bayani Akan Wanda Ya Kamu Da Cutar Korona A Jihar Jigawa \u2013 AREWA News"},"content":{"rendered":"<div itemprop=\"articleBody\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"wp-image-38240 size-full aligncenter\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/04\/Bayani-Akan-Wanda-Ya-Kamu-Da-Cutar-Korona-A-Jihar-Jigawa-\u2013-AREWA-News.jpg\" width=\"480\" height=\"318\" data-temp-aztec-id=\"c53612f6-ad5a-4384-88c4-9a833d27f6a5\"><\/p>\n<p>Gwamnatin Jihar Jigawa ta tsinkayi jita-jita dake ta yawo akan an samu \u0253ullar cutar Korona Bairos a Jihar Jigawa, wanda hakan ke ta yawo musamman a Kafafen Sadarwa.<\/p>\n<p>Duk da cewa hakika wanda ake magana a kansa \u0257an asalin Jihar Jigawa ne, amma gwajin da ya tabbatar da cewa yana \u0257auke da cutar da sakamakon gwajin ba a gudanar da shi a Jihar Jigawa ba.<\/p>\n<p>Wanda aka samu \u0257auke da cutar ya kasance Fasinja ne da ya taso daga Jihar Legas zuwa Jigawa, da shi da \u0257an uwansa, inda suka biyo ta Kano, a yayin da suka iso kan iyakar Kano aka tare su, inda Jami\u2019an Ya\u0199i da Cutar Covid-19 ta Jihar Kano ta killace su, ta kuma gwada lafiyar su, inda daga bisani aka tabbatar \u0257aya daga cikin fasinjan na \u0257auke da cutar ta covid-19.<\/p>\n<p>Abin takaici da ya janyo hankalin Gwamnatin Jihar Jigawa take \u0199arin haske akan wannan batu, shine tuburewa da Gwamnatin Jihar Kano tayi na mi\u0199awa Jihar Jigawa wanda aka samu yana \u0257auke da wannan cuta.<\/p>\n<p>Sanin kowa ne, inda da yawa suka yabawa Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, tun farko bai yi \u0199asa a gwiwa ba wajen tunkarar wannan cuta gadan-gadan ba, inda ya tanadar da matakai da kafa kwamiti da zasu da\u0199ile ya\u0257uwar wannan annoba a Jihar Jigawa, tare da tabbatar da samar da tallafi domin ragewa al\u2019uma ra\u0257a\u0257i, hana ma\u2019aikata zuwa wajen aiki, ta\u0199aita zirga-zirga da yin feshi.<\/p>\n<p>A cikin gwamnoni 36 da muke da su a \u0198asar nan, Gwamna Badaru yana cikin sahun farko na gwamnoni da takwarorin sa na Arewa maso Yamma, da suka \u0257auki matakin rufe makarantu na kwanaki 30 tun daga 23 ga watan Maris, domin da\u0199ile ya\u0257uwar cutar.<\/p>\n<p>Duk da haka, idan zamu iya tunawa, Kontirola Janar na Hukumar Shige da Fice na Najeriya Muhammad Babandede, wanda \u0257an asalin Jihar Jigawa ne ya kamu da wannan cuta, amma hakan bai sa Birnin Tarayya ko Hukumar NCDC tasa tace Jihar Jigawa nada wa\u0257anda ke \u0257auke da wannan cuta ba, don ba a Jihar Jigawa aka yi masa gwaji ba, kuma da sakamakon sa ya fito ba a ce a dawo da shi Jihar Jigawa a killace shi ba.<\/p>\n<p>A dalilin haka ne, Gwamnatin Jihar Jigawa ke \u0199ara tabbatarwa da duniya cewa, Jihar bata da ko da mutum \u0257aya dake \u0257auke da wannan cuta a fa\u0257in Jihar a hukumance.<\/p>\n<p>Dagewa da Gwamnatin Jihar Kano tayi na a dawowa Jihar Jigawa da waccan mutumin da aka samu da wannan cutar ne, yasa Gwamna Badaru ya bada umarni Jami\u2019an Ma\u2019aikatar lafiya su tafi Kano su \u0257auko mara lafiyan, inda tuni an kawo shi Dutse, inda aka killace shi a wurin da aka tanadar, kuma tuni ya fara kar\u0253an magani.<\/p>\n<p>Jihar Jigawa zata cigaba da bibiya, nuna damuwa da kuma zama cikin shirin dawowa da duk wani \u0257an asalin Jihar Jigawa da Allah ya jarrabe shi, a yayin da aka \u0199i kar\u0253arsa ko aka \u0199yamaceshi a inda yake.<\/p>\n<p>A wannan ga\u0253ar ne, ake kiran jama\u2019a da kar su yarda da wannan labari don a jihar Jigawa ba a samu dlmai \u0257auke da wannan cuta ba, kuma har yanzu babu wani wanda ake zargi da wannan cuta.<\/p>\n<p>Gwamna Badaru, yana kuma kira ga al\u2019umar Jihar Jigawa da su \u0199ara kwantar da hankalin su, kada su tsorata, inda ya \u0199ara tabbatar musu da cewa zai cigaba da iya \u0199o\u0199arin sa na da\u0199ile ya\u0257uwar cutar a Jihar Jigawa.<\/p>\n<p>Gwamna Badaru yace Ya\u0199i akan da\u0199ile cutar Korona Bairos, Ya\u0199i ne na kowa da kowa, don haka ne ya nemi al\u2019umar Jihar su cigaba da wanke hannayen su akai akai, abi umarnin Ma\u2019aikatar Lafiya, kuma a ta\u0199aita zirga zirga da cigaba da nesanta kai da cu\u0257anya da mutane.<\/p>\n<p>Auwal D. Sankara (Fica),<br \/>\n(Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa)<\/p>\n<p><!-- --><\/p>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Gwamnatin Jihar Jigawa ta tsinkayi jita-jita dake ta yawo akan an samu \u0253ullar cutar Korona Bairos a Jihar Jigawa, wanda hakan ke ta yawo musamman a Kafafen Sadarwa. Duk da cewa hakika wanda ake magana a kansa \u0257an asalin Jihar Jigawa ne, amma gwajin da ya tabbatar da cewa yana \u0257auke da cutar da sakamakon [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":211075,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681,14571],"tags":[10087,14173,236],"class_list":["post-211074","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","category-health","tag-badaru","tag-coronavirus","tag-jigawa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/211074","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=211074"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/211074\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/211075"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=211074"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=211074"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=211074"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}