{"id":207463,"date":"2020-04-06T08:31:14","date_gmt":"2020-04-06T07:31:14","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=207463"},"modified":"2020-04-06T08:32:27","modified_gmt":"2020-04-06T07:32:27","slug":"coronavirus-gwamnatin-neja-ta-ce-a-koma-bakin-aiki-bbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=207463","title":{"rendered":"Coronavirus: Gwamnatin Neja ta ce a koma bakin aiki | BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-with-caption\">\n<div class=\"player-with-placeholder\"><img decoding=\"async\" class=\"media-placeholder player-with-placeholder__image narrative-audio-placeholder\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/04\/Coronavirus-Gwamnatin-Neja-ta-ce-a-koma-bakin-aiki.jpg\"><\/p>\n<p>Na&#8217;urarku na da matsalar sauraren sauti<\/p><\/div><figcaption class=\"media-with-caption__caption\">Latsa alamar lasifikar domin sauraron jawabin Kwamishinan yada labaran jihar Neja a tattaunawarsu da Haruna Shehu Tangaza<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Gwamnatin Neja da ke tsakiyar Najeriya ta sanar da matakin sassauta umarnin hana fita da ta sanya tun bayan bullar annobar coronavirus a kasar.<\/p>\n<p>Kwamishinan watsa labarai na jihar, Alhaji Sani Idris ya shaida wa BBC cewa tun da farko dai gwamnatin ta ba da umarnin hana tafiye-tafiye daga karfe takwas na safe zuwa takwas na yamma domin kare yada cutar.<\/p>\n<p>A cewar kwamishinan, sauran dokokin da aka sa kamar na hana taruwa a makaranta da wuraren ibada suna nan daram.<\/p>\n<p>Har yanzu dai ba a samu rahoton bullar cutar coronavirus ba a jihar duk da cewa jihar na makwabtaka da Abuja babban birnin kasar.<\/p>\n<p>Ya ce gwamnati ta sha sassauta dokar hana fitar a lokuta daban-daban sakamakon bibiyar al&#8217;amuran da ke wakana a Abuja.<\/p>\n<p>&#8220;Daga baya mun yi sassauci aka mayar da dokar daga karfe goma na safe zuwa takwas na dare sannan da muka ga iyakoki a bude ana shige da fice, sai muka sake mayar da dokar daga karfe goma na safe zuwa 12 na dare,&#8221;.<\/p>\n<p>A cewarsa, tun daga lokacin gwamnatin jihar ta bijiro da tsare-tsare daban-daban da suka hadar da gudanar da bincike kan baki da suka shiga jihar.<\/p>\n<p>&#8220;La&#8217;akari da yadda al&#8217;umma suka ba da goyon baya muka ga ya kamata a kara sassauta dokar,&#8221;. Kwamishinan ya ce matakin zai bai wa gwamnati damar fito da tsare-tsare masu muhimmanci.<\/p>\n<p>&#8220;Akwai umarni da aka ba shugabannin ma&#8217;aikatun da za a bude, kowace ma&#8217;aikata za a tanadi abubuwa da ma&#8217;ikatan lafiya suka ba da shawara yadda za a wanke hannu da kiyaye cunkoso.&#8221;<\/p>\n<p>&#8220;Matakin dakatar da tafiye-tafiye tsakanin makwabtan jihohi zuwa Neja har yanzu yana nan.&#8221;<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Na&#8217;urarku na da matsalar sauraren sautiLatsa alamar lasifikar domin sauraron jawabin Kwamishinan yada labaran jihar Neja a tattaunawarsu da Haruna Shehu Tangaza Gwamnatin Neja da ke tsakiyar Najeriya ta sanar da matakin sassauta umarnin hana fita da ta sanya tun bayan bullar annobar coronavirus a kasar. Kwamishinan watsa labarai na jihar, Alhaji Sani Idris ya [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":207464,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[1],"tags":[5550,14640],"class_list":["post-207463","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-more","tag-abubakar-sani-bello","tag-neja"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/207463","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=207463"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/207463\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/207464"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=207463"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=207463"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=207463"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}