{"id":203094,"date":"2020-03-20T08:02:28","date_gmt":"2020-03-20T07:02:28","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=203094"},"modified":"2020-03-20T08:03:06","modified_gmt":"2020-03-20T07:03:06","slug":"ya-kamata-afirka-ta-shirya-zuwan-mummunar-annoba-who","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=203094","title":{"rendered":"Ya kamata Afirka ta shirya zuwan mummunar annoba \u2014 WHO"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Wani jami'in lafiya na gwada zafin jikin mutane a filin jirgin saman kasar Habasha\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/03\/Sai-Afirka-ta-shirya-zuwan-mummunar-annoba-\u2014-WHO.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">AFP<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nAfrica ana gwaji a yawancin filayen jiragen sama na kasashen Afirka<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Shugaban hukumar lafiya ta duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce yakamata Afirka ta tashi tsaye don tunkarar munin halin da za a shiga sakamakon annobar coronavirus tare da shirya yaki da ita.<\/p>\n<p>Ya kamata nahiyar ta lura da yadda cutar ke saurin yaduwa in ji Tedros Adhanom Ghebreyesus.<\/p>\n<p>Shugaban ya yi gargadin cewa duk da kasancewar babu masu fama da cutar sosai a nahiyar, amma ya kamata a dauki matakin da ya dace wajen hana yaduwarta.<\/p>\n<p>Mr Ghebreyesus ya ce &#8221; Afirka ku tashi, nahiyata ku farka domin dakile yaduwar coronavirus&#8221;.<\/p>\n<p>Kwararru a bangaren lafiya sun yi gargadin cewa matsalar da kasashen Afirka ke fama da ita ta rashin isassun kayayyakin kula da marasa lafiya na iya ta&#8217;azzara idan cutar ta ci gaba yaduwa musamman a wajen taron jama&#8217;a.<\/p>\n<p>Hukumar lafiya ta duniyar ta bayar da shawarar a guji shiga tarukan jama&#8217;a.<\/p>\n<p>A Afirka, ya zuwa yanzu mutum 16 sun mutu sakamakon kamuwa da cutar coronavirus inda mutum 6 suka fito daga kasar Masar, 6 daga Algeria, biyu daga Morocco daya a Sudan sannan daya a Burkina Faso.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">AFP<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTedros Adhanom Ghebreyesus<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>A Afirka ta Kudu, inda aka samu mutum 116 da suka kamu, shugaban kasar Cyril Ramaphosa ya ayyana cewa ana cikin babban bala&#8217;i saboda bullar covid-19, don haka ya takaita tafiye-tafiye, aka kuma rufe makarantu, da hana taruka tare da rufe gidajen barasa.<\/p>\n<p>Kazalika kasar ta kuma dakatar da zirga-zirgar jiragen ruwa.<\/p>\n<p>An sanya hukuncin zaman gidan yari ko biyan tara a Afirka ta Kudu ga duk wanda ya karya ka&#8217;idojin da aka shimfida na yaki da coronavirus a kasar.<\/p>\n<p>Akwai wasu kasashen Afirkan da su ma suka sanya takunkumai makamantan na Afirka ta Kudu.<\/p>\n<p>Jihar Lagos cibiyar kasuwancin Najeriya, ta haramta gudanar da tarukan da suka wuce na mutum 50, sannan za a rufe makarantu daga mako mai zuwa.<\/p>\n<p>Kazalika Najeriya ma wadda ya zuwa yanzu take da mutum 12 da suka kamu da cutar, ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama daga kasashen da cutar ta yi kamari.<\/p>\n<p>Ita kuwa Algeria, wato daya daga cikin kasashen Afirkan da cutar ta fi yawa, ta rufe dukkan iyakokinta sannan ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Reuters<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>Haka an haramta gudanar da tarukan jama&#8217;a a kasar.<\/p>\n<p>Rwanda, wadda ke da mutum 11 da suka kamu da cutar za ta hana shiga kasarta daga ranar Jumma&#8217;a 20 ga watan Maris har tsawon wata guda.<\/p>\n<p>Kenya, ta dakatar da sallah a masallatai tare da hana gudanar da ibada a majami&#8217;u, sannan kasar ta ce za ta samar da sinadarin goge hannun don rabawa kyauta ga &#8216;yan kasar.<\/p>\n<p>Liberia, wadda ta sha fama da cutar Ebola a shekarun baya, tana da mutum biyu da suka kamu da coronavirus, kuma ta hana bayar da visa domin dakatar da tafiye-tafiye a tsakanin &#8216;yan kasar.<\/p>\n<p>Kazalika ta hana &#8216;yan wasu kasar shiga kasarta.<\/p>\n<p>Zambia, wadda ke da mutum biyu da suka kamu da cutar ta dakatar da taron majalisun kasar tare da rufe makarantu da jami&#8217;o&#8217;i.<\/p>\n<p>Somalia mai mutum guda ta rufe sararin samaniyarta.<\/p>\n<p>Uganda da Botswana ba su samu bullar cutar a kasashensu ba ya zuwa yanzu amma duk da haka za su rufe makarantu daga mako mai zuwa.<\/p>\n<p>Chadi wadda aka samu mutum guda da coronavirus ta harba, ta dakatar da zirga-zirgar jiragen fasinja tare da kulle iyakokinta na tudu.<\/p>\n<figure class=\"media-portrait no-caption full-width\">\n<\/figure>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\"><\/figure>\n<\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto AFP Image caption Africa ana gwaji a yawancin filayen jiragen sama na kasashen Afirka Shugaban hukumar lafiya ta duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce yakamata Afirka ta tashi tsaye don tunkarar munin halin da za a shiga sakamakon annobar coronavirus tare da shirya yaki da ita. Ya kamata nahiyar ta lura da [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":203095,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[1],"tags":[14052,1795,1147,1968],"class_list":["post-203094","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-more","tag-corona-virus","tag-un","tag-unicef","tag-who"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/203094","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=203094"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/203094\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/203095"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=203094"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=203094"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=203094"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}