{"id":194362,"date":"2020-02-17T14:33:46","date_gmt":"2020-02-17T13:33:46","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=194362"},"modified":"2020-02-17T14:34:00","modified_gmt":"2020-02-17T13:34:00","slug":"an-kashe-mutum-22-a-wani-kauyen-kamaru","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=194362","title":{"rendered":"An kashe mutum 22 a wani kauyen Kamaru"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Kamaru\" src=\"https:\/\/arewa.ng\/storage\/2020\/02\/An-kashe-mutum-22-a-wani-kauyen-Kamaru.png\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Majalisar Dinkin Duniya MDD ta ce kimanin mutum 22 ne suka mutu a wani hari da aka kai wani kauye da ke arewa maso yammacin Kamaru.<\/p>\n<p>Sama da rabin mutanen da aka kashe a Ntumbo yara ne, kuma kafafen yada labaran kasar sun ce wasu da dama sun kone kurmus.<\/p>\n<p>Babu kungiyar da ta dauki nauyin kai harin na ranar Juma&#8217;a, sai dai jam&#8217;iyyar hamayya na zargin rundunar sojin kasar.<\/p>\n<p>Gwamnatin Kamaru wadda take yaki da &#8216;yan aware a yankin kusan shekara uku kenan ta musanta hannu a harin.<\/p>\n<p>James Nuna, wani jami&#8217;i daga hukumar ba da agaji ta MDD Ocha, ya fada wa BBC cewa wata mata mai juna biyu na daga cikin mutanen da aka kashe.<\/p>\n<p>&#8220;Yara 14 ciki har da &#8216;yan kasa shekara biyar su tara, na daga cikin wadanda suka mutu,&#8221; a cewarsa.<\/p>\n<p>Mr Nunan ya ce lamarin ya tayar da hankalin al&#8217;ummar yankin.<\/p>\n<p>&#8221;Kowace kungiya ce ta yi haka ta yi barazanar kara tayar da hankali a gaba,&#8221; a cewarsa. &#8221;Mutanen da muka yi magana da su sun kadu matuka kuma ba su yi tsammanin faruwar haka ba.&#8221;<\/p>\n<p>Cikin wata sanarwa, daya daga cikin manyan jam&#8217;iyyun hamayyar kasar &#8211; MRC &#8211; ta zargi gwamnatin kama karya da kuma shugaban dakarun kasar da kai harin.<\/p>\n<p>Agbor Mballa wani babba a kungiyar &#8216;yan awaren ya ce sojojin kasar ne da alhakin kai harin.<\/p>\n<p>Wani jami&#8217;in soji kuma ya karyata zarge-zargen lokacin da kamfanin dillancin labaran AFP ya tambaye shi game da lamarin.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\"><figcaption class=\"media-caption\"><span class=\"media-caption__text\">An sha zargin Shugaban Kamaru Biya da take hakkokin bil adama a lokacin rikici<\/span><br \/>\n<\/figcaption>Rikicin na faruwa ne a arewa maso yammacin Kamaru inda akasarin jama&#8217;ar yankin ke Ingilishi saboda dadaddiyar alaka da Birtaniya.<\/figure>\n<p>Kungiyoyin &#8216;yan aware sun fara kafuwa a 2017 bayan da sojoji suk afkawa masu zanga-zanga.<\/p>\n<p>&#8216;Yan awaren sun ayyana cin gashin kansu a sabuwar jihar Ambazonia, sai dai shugaban kasar Paul Biya ya bayyana su a matsayin &#8216;yan ta&#8217;adda.<\/p>\n<p>Sama da mutum 3,000 ne suka mutu tun bayan barkewar rikici kuma kimanin mutum 70,000 ne sukarasa muhallansu.<\/p>\n<p>Ana zargin gwamnatin Kamaru da cin zarafin bil adama a lokacin yaki kuma Shugaban Amurka Donald Trump ya tsame kasar daga wani shirin kasuwanci na musamman.<\/p>\n<p>Gwamnati ta ce &#8216;yan awaren sun kashe farar hula da sojoji da dama amma babu kididdiga a hukumance kan yawan farar hula da &#8216;yan waren da sojoji suka kashe.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Majalisar Dinkin Duniya MDD ta ce kimanin mutum 22 ne suka mutu a wani hari da aka kai wani kauye da ke arewa maso yammacin Kamaru. Sama da rabin mutanen da aka kashe a Ntumbo yara ne, kuma kafafen yada labaran kasar sun ce wasu da dama sun kone kurmus. Babu kungiyar da ta dauki [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":194363,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":false,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[14313],"class_list":["post-194362","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-kamaru"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/194362","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=194362"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/194362\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/194363"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=194362"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=194362"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=194362"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}