{"id":150612,"date":"2019-09-09T07:41:49","date_gmt":"2019-09-09T06:41:49","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=150612"},"modified":"2019-09-09T07:42:16","modified_gmt":"2019-09-09T06:42:16","slug":"amurka-ba-ta-da-kwarewa-inji-taliban","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=150612","title":{"rendered":"Amurka ba ta da kwarewa, inji Taliban"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\">\n<p><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Hibatullah Akhundzada shi ne sabon shugaban Taliban a Afghanistan\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/09\/Taliban-ta-ce-Amurka-ba-ta-da-kwarewa.png\" width=\"976\" height=\"549\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nHibatullah Akhundzada, tsohon shugaban kotunan Taliban, shi ne sabon shugaban kungiyar a Afghanistan,<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Kungiyar Taliban ta mayar da martani kan matakin Shugaba Trump na yin watsi da yarjejeniyar zaman lafiya a Afghanistan, tare da fasa ganawar sirri da ya shirya yi da shugabannin kungiyar a Amurka.<\/p>\n<p>Shugaban ya dauki matakin ne bayan wani wawan hari da kungiyar ta kai ranar Alhamis wanda ya hallaka mutane 12 ciki har da sojan Amurka daya.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTaliban ta kai hare-hare da dama a Afghanistan ciki har da na majalisar dokokin kasar a watan Yuni na 2015<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>A martanin kungiyar ta ce matakin shugaban ya nuna rashin kwarewa da kuma aniyar Amurka kan rikicin na Afghanistan;<\/p>\n<p>A martanin nata kungiyar Taliban ta ce komai na tafiya lami lafiya kafin Shugaba Trump ya soke ganawarsu.<\/p>\n<p>A sanarwar da kungyar ta fitar ta ce, an gayyaci shugabanninta zuwa Amurka a karshen watan Agusta, amma suka jinkirta har sai an kammala sanya hannu a yarjejeniyar da ake yi. Haka su ma kasashen yankin sun mara baya ga hakan.<\/p>\n<p>Kungiyar ta ce tun da yanzu shugaban Amurkar ya soke tattaunawar zaman lafiyar, Amurka ce za ta fi yin asara, za ta rasa kimarta, sannan a yanzu za a kara sanin matsayi da manufarta kan batun zaman lafiya, wato za a san cewa ba da gaske take ba.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nAkwai kungiyoyin mayaka daban-daban na Taliban<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>A sanarwar Taliban ta ce, a bangarensu, sun tabbatar cewa, yaki dai kai musu shi aka yi, kuma a duk lokacin da ake da niyyar tattaunawa, a shirye suke.<\/p>\n<p>Ta ce ficewa daga tattaunawar zaman lafiya kafin sanya hannu a yarjejeniyar, saboda hari ko fashewa daya kawai, hakan ya nuna rashin hakuri ko kwarewar Amurka, musamman ma a lokacin da rayuka da dukiyar tarin &#8216;yan Afghanistan suka salwanta a sanadiyyar hare-haren Amurka da kawayenta a Afghanistan.<\/p>\n<p>Taliban din ta ce, tana da kwakkwarar manufa da zaman lafiya, domin shekara ashirin baya ta ce ta nemi a zauna a tattauna, kuma har a yau din nan a shirye take da hakan.<\/p>\n<p>A karshe sun ce sun yi amanna, nan ba da jimawa ba Amurkawan ma za su cimma wannan matsaya.<\/p>\n<p>Matakin na Shugaba Trump ya kasance tamkar wata babbar mahangurba ga shirin wanzar da zaman lafiyar a Afghanistan, matakin da harin da &#8216;yan Taliban suka kai wanda ya harzuka shugaban kasancewar akwai sojan Amurka daya tilo daga cikin mutum 12 da harin na Kabul ya hallaka a ranar Alhamis.<\/p>\n<p>Tattaunawar yarjejeniyar dai na wakana lafiya kalau, da har da dama daga jama&#8217;ar Afghanistan na murna da ganin ana dab da kawo karshen rikicin da kusan a kullum ke musu taannati na rayuka da dukiya da zaman lafiya shekara da shekaru.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Image caption Hibatullah Akhundzada, tsohon shugaban kotunan Taliban, shi ne sabon shugaban kungiyar a Afghanistan, Kungiyar Taliban ta mayar da martani kan matakin Shugaba Trump na yin watsi da yarjejeniyar zaman lafiya a Afghanistan, tare da fasa ganawar sirri da ya shirya yi da shugabannin kungiyar a Amurka. Shugaban ya dauki matakin ne bayan wani [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":150613,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[9075,12349,5894],"class_list":["post-150612","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-afghanistan","tag-taliban","tag-trump"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/150612","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=150612"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/150612\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/150613"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=150612"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=150612"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=150612"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}