{"id":149866,"date":"2019-09-06T08:20:34","date_gmt":"2019-09-06T07:20:34","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=149866"},"modified":"2019-09-06T08:21:05","modified_gmt":"2019-09-06T07:21:05","slug":"najeriya-za-ta-karbo-yayan-mayakan-kungiyar-is","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=149866","title":{"rendered":"Najeriya za ta karbo &#8216;ya&#8217;yan mayakan kungiyar IS"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\">\n<p><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Mayakan IS\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/09\/Najeriya-za-ta-karbo-yayan-mayakan-kungiyar-IS.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Najeriya za ta kasance kasar farko da ta karbi yara marayu masu alaka da mayakan kungiyar &#8216;yan ta-da-kayar-baya ta IS a Afirka.<\/p>\n<p>Kamfanin dillancin labaran AFP ya ruwaito cewa wani jami&#8217;i ne ya karbi wadannan yara daga hannun mahukuntan Kurdawa a madadin gwamnatin Nijeriya.<\/p>\n<p>Yaran kuma sun hadar da mace daya da namiji biyu, wadanda shekarunsu suka kama daga biyar zuwa 10.<\/p>\n<p>Kuma an ambato shi jami&#8217;in na cewa gwamnatin Nijeriya tana bibiyar k&#8217;arin wasu batutuwa na irin wadannan yara, da ke hannun Kurdawa.<\/p>\n<p>Mai magana da yawun gwamnatin Nijeriya Mallam Garba Shehu ya shaida wa BBC halin da ake ciki.<\/p>\n<p>Jami&#8217;in mai suna Musa Habib ya ce sun bukaci ma&#8217;aikatar hulda da kasashen wajen Kurdawa ta ba su jerin sunayen yaran da mahaifansu suka fito daga Nijeriya da ma sauran kasashen Afirka da ke hannunta.<\/p>\n<p>Malam Garba Shehu, ya ce gwamnatin kasar na ci gaba da tuntubar ofishin jakadancin Nijeriya da ke Lebanon don samun tabbaci ko yaran uku, &#8216;ya&#8217;yan dan Nijeriyan nan da aka yi zargin cewa ya je Siriya don yaki a karkashin kungiyar &#8216;yan ta-da-kayar-bayan IS, Ibrahim Uwais.<\/p>\n<p>Hatta a lokacin da mayakan Kurdawa ke yaki da sauran &#8216;yan ta-da-kayar-bayan da suka shiga fadan sari-ka-nok&#8217;e, akwai dubban mayak&#8217;an IS da iyalansu da ke tsare a hannunsu.<\/p>\n<p>Daga ciki kuma daruruwan mayakan da ake zargi &#8216;yan kasashen waje ne wadanda ke tsare a gidajen yari, da kuma dubban iyalansu da ke cunkushe a sansanoni.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nMata da kananan yara ne suka fi shan wuya a duk lokacin da ake yaki<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Kasashen Yamma da dama dai na nuna kin amincewa su karbi mutanen kasashensu.<\/p>\n<p>Amma Jamus da Faransa da Beljiyum sun karbi kalilan daga cikin irin wadannan marayu inda suka mayar da su gida.<\/p>\n<p>Ko a bara ma sai da Amurka ta karbi wata mata da &#8216;ya&#8217;yanta hudu da suka fito daga kasar.<\/p>\n<p>Haka zalika kasashen Kazakhstan da Uzbekistan da Kosovo su ma tuni sun mayar da gomman mata da kananan yara &#8216;yan kasashensu zuwa gida.<\/p>\n<p>Mayakan Kurdawa dai su ne suka jagoranci yak&#8217;i da kungiyar IS da goyon bayan Amurka a Siriya.<\/p>\n<p>A watan Maris din wannan shekara ne suka fatattaki &#8216;yan ta-da-kayar-bayan daga wani yankin na karshe da suke rik&#8217;e da shi a wannan kasa da yak&#8217;i ya daidaita.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Najeriya za ta kasance kasar farko da ta karbi yara marayu masu alaka da mayakan kungiyar &#8216;yan ta-da-kayar-baya ta IS a Afirka. Kamfanin dillancin labaran AFP ya ruwaito cewa wani jami&#8217;i ne ya karbi wadannan yara daga hannun mahukuntan Kurdawa a madadin gwamnatin Nijeriya. Yaran kuma sun hadar da mace [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":149867,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[4797,12415],"class_list":["post-149866","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-fg","tag-iswap"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/149866","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=149866"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/149866\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/149867"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=149866"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=149866"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=149866"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}