{"id":144297,"date":"2019-08-17T06:12:16","date_gmt":"2019-08-17T05:12:16","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=144297"},"modified":"2019-08-17T06:13:26","modified_gmt":"2019-08-17T05:13:26","slug":"zakzaky-ya-so-kunyata-najeriya-da-indiya-a-idon-duniya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=144297","title":{"rendered":"&#8216;Zakzaky ya so kunyata Najeriya da Indiya a idon duniya&#8217;"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Ana tsare da Sheikh Zakzaky tun 2015\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/08\/Gwamnatin-Najeriya-Sheikh-Ibrahim-El-Zakzaky-ya-so-kunyata-Najeriya-da-Indiya-a-idon-duniya.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Gwamnatin Najeriya ta ce wasu dabi&#8217;u da shugaban kungiyar harka Isalamiyya na Najeriya ya nuna a kasar Indiya da ka iya kunyata gwamnatocin Najeriya da India na daga cikin dalilan da suka sanya aka mayar da shi gida.<\/p>\n<p>A ranar Juma&#8217;a 16 ga watan Agusta ne dai Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya isa Najeriya bayan yunkurin kula da lafiyarsa da mai dakinsa Zeenat ya ci tura a kasar Indiya.<\/p>\n<p>Malamin dai a cikin wani sako da ya fitar ta faifan bidiyo gabanin komawarsa Najeriya, ya ce yana ganin ba zai samu kulawar da ta dace ba, kasancewar ba a bar shi ya gana da likitocin da suka cancanta ba.<\/p>\n<p>Sannan gabanin hakan ya yi zargin cewa an tsananta tsaro a asibitin da yake zaune, inda ya ce akwai matukar takura ga rayuwarsa.<\/p>\n<p>Sai dai bayan komawar malamin Najeriya, kamfanin dillancin labaru na Najeriya ya ruwaito cewa babbar sakatariyar ma&#8217;aikatar yada labarun kasar, Mrs. Grace Gekpe ta ce halayyar da Sheikh Zakzaky ya nuna a kasar ta India ne ta sanya dole a mayar da shi gida.<\/p>\n<p>A cewar wata sanarwar da ta fitar &#8220;A wani yunkuri na wancakali da ka&#8217;idoji na kasa da kasa, jagoran na IMN ya fara tuntubar wasu lauyoyi a Indiya da nufin neman mafaka a kasar&#8221;.<\/p>\n<p>&#8220;Ya kuma tuntubi wasu kungiyoyi masu zaman kansu kamar hukumar kare hakkin dan&#8217;adam ta muslunci, da wasu kungiyoyi masu alaka da akidar Shi&#8217;a domin ganin ya samu nasarar neman mafakar&#8221;.<\/p>\n<p>Sanarwar ta yi bayanin cewa inda Sheikh Ibrahim Zakzaky ya samu nasarar samun umurnin kotu a kasar Indiya na neman mafaka, to da hakan ya saba wa ka&#8217;idojin da kotu ta gindaya a Najeriya game da shari&#8217;ar da ake masa.<\/p>\n<p>Bugu da kari sanarwar ta zargi matar Sheikh Zakzaky, Zeenat, da laifin kokarin haifar da rashin jituwa tsakanin jami&#8217;an tsaron Najeriya da na Indiya, a lokacin da ta zargi jami&#8217;an tsaron Najeriya da laifin kisan &#8216;yayanta.<\/p>\n<figure class=\"media-portrait no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">@SZAKZAKYOFFICE<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>Ita dai gwamnatin Najeriya ta yi kokarin bin umurnin wata babbar kotu ne ta jihar Kaduna, wadda ta amince wa Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da matarsa Zeenat su tafi kasar Indiya domin neman lafiya.<\/p>\n<p>Malamin yana fama ne da rashin lafiya tun bayan kama shi da aka yi da matarsa a shekara ta 2015, bayan wani artabu tsakanin mabiya malamin da kuma jami&#8217;an tsaron Najeriya.<\/p>\n<p>Sai dai an samu rashin jituwa bayan isar malamin kasar Indiya domin neman magani, inda malamin ya ki amincewa da likitocin da asibitin Medanta ta wakilta domin duba lafiyarsa.<\/p>\n<p>Tun a shekara ta 2015 ne dai ake tsare da malamin, inda ake tuhumarsa da wasu jerin laifuka a gaban kotu.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Gwamnatin Najeriya ta ce wasu dabi&#8217;u da shugaban kungiyar harka Isalamiyya na Najeriya ya nuna a kasar Indiya da ka iya kunyata gwamnatocin Najeriya da India na daga cikin dalilan da suka sanya aka mayar da shi gida. A ranar Juma&#8217;a 16 ga watan Agusta ne dai Sheikh Ibrahim El-Zakzaky [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":144298,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[11057,7011,4797,581],"class_list":["post-144297","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-elrufai-2","tag-elzakzaky","tag-fg","tag-shiite"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/144297","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=144297"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/144297\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/144298"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=144297"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=144297"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=144297"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}