{"id":141969,"date":"2019-08-08T06:59:06","date_gmt":"2019-08-08T05:59:06","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=141969"},"modified":"2019-08-08T06:59:48","modified_gmt":"2019-08-08T05:59:48","slug":"sojoji-sun-kashe-yan-sanda-uku-a-taraba-bbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=141969","title":{"rendered":"Sojoji sun kashe &#8216;yan sanda uku a Taraba | BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Sojojin Najeriya\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/08\/Sojoji-sun-kashe-yan-sanda-uku-a-Taraba.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">others<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nSojojin sun kuma kubutar da wanda &#8216;yan sandan suka kama wanda &#8216;kasurgumin mai satar mutane ne&#8217;<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Rundunar &#8216;yan sanda ta Najeriya ta ce wasu sojojin kasar sun hallaka jami&#8217;anta uku tare da raunata wasu bayan da sojojin suka bude wa wata tawagar &#8216;yan sandan wuta a jihar Taraba.<\/p>\n<p>Lamarin ya faru ne a kan hanyar Ibi zuwa Jalingo, kamar yanda wata sanarwa da &#8216;yan sandan suka fitar ta bayyana cewa tawagar ta masu kai daukin gaggawa ce ta Intelligence Response Team (IRT).<\/p>\n<p>Sanarwar ta ce tawagar tana karkashin jagorancin Felix Adolije, mataimakin sufuritanda na &#8216;yansanda, inda ta je jihar domin kama wani da ake kira Alhaji Hamisu, wanda ake zargi da cewa kasurgumin mai satar mutane ne.<\/p>\n<p>Daga nan ne sai kawai wasu &#8220;sojoji na Najeriyar suka bude wa tawagar wuta ba kakkautawa&#8221;, kamar yadda sanarwar da ta fito daga kakakin rundunar &#8216;yan sandan ta kasa, Frank Mba, ta bayyana.<\/p>\n<p>Sanarwar ta kara da cewa jami&#8217;an &#8216;yan sandan sun kama mutumin ne za su kai shi hedikwatar &#8216;yan sanda ta jihar a Jalingo lokacin da sojojin suka bude musu wuta, duk kuwa da cikakkiyar shedar da ke nuna cewa suna kan aikinsu.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTuni Babban-Sufeton &#8216;yan sandan Najeriya Muhammad Adamu ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan lamarin<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Bayan &#8216;yan sandan, lamarin ya kuma rutsa da ran wani farar hula, da sufeto da kuma wasu &#8216;yan sandan biyu masu mukamin saja, yayin da wasu &#8216;yan sandan kuma da ba a bayyana yawansu ba suka samu raunuka.<\/p>\n<p>Sanarwar ta ce bayan nan ne sai sojojin suka &#8220;kubutar da wanda ake zargin&#8221;, abin da ya sa ya tsere, har yanzu ba a san inda yake ba.<\/p>\n<p>&#8216;Yan sandan suna zargin mutumin, Alhaji Hamisu da kasancewa kasurgumin mai satar mutane, da suka dade suna nema saboda hannu a sace-sacen jama, ciki har na sace wani dan kasuwa mai harkar mai da aka yi kwanan nan a jihar ta Taraba.<\/p>\n<p>Dan kasuwar mai sayar da mai wanda ba a bayyana sunansa ba a sanarwar, an ce sai da ya biya naira miliyan 100 aka sako shi.<\/p>\n<p>Tuni aka tura wani mataimakin sufeto-janar na &#8216;yan sanda domin tsara yadda za a yi wa wadanda aka jikkata magani, yayin da kuma aka ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a asibiti.<\/p>\n<p>Shugaban rundunar &#8216;yan sanda ta kasa Muhammad Adamu ya bayar da umarnin gudanar da binciken gaggawa kan lamarin, in ji kakakin rundunar ta kasa Mista Frank Mba, mai mukamin mataimakin kwaminishinan &#8216;yan sanda.<\/p>\n<p>Sai dai kuma babu wani martani kawo yanzu daga hukumomin sojin Najeriyar dangane da zargin na &#8216;yan sanda.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto others Image caption Sojojin sun kuma kubutar da wanda &#8216;yan sandan suka kama wanda &#8216;kasurgumin mai satar mutane ne&#8217; Rundunar &#8216;yan sanda ta Najeriya ta ce wasu sojojin kasar sun hallaka jami&#8217;anta uku tare da raunata wasu bayan da sojojin suka bude wa wata tawagar &#8216;yan sandan wuta a jihar Taraba. Lamarin [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":141970,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[1],"tags":[11064,11283,1126,4716,270],"class_list":["post-141969","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-more","tag-burutai","tag-darius-i-ishaku","tag-nigerian-army","tag-npf","tag-taraba"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/141969","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=141969"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/141969\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/141970"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=141969"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=141969"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=141969"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}