{"id":136849,"date":"2019-07-19T07:52:28","date_gmt":"2019-07-19T06:52:28","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=136849"},"modified":"2019-07-19T07:52:50","modified_gmt":"2019-07-19T06:52:50","slug":"afcon-yan-algeria-5000-sun-daga-wa-masar-hankali","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=136849","title":{"rendered":"AFCON: &#8216;Yan Algeria 5,000 sun daga wa Masar hankali"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Algerian fan shows the Egyptian flag during the semi-final match against Nigeria\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/07\/AFCON-Yan-Algeria-5000-sun-daga-wa-Masar-hankali.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nShin &#8216;yan Aljeriya da Masar sun warware rashin jituwar da ke tsakaninsu a fagen kwallon kafa?<\/span><br \/>\n&#8212;BBC Hausa<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Labarin cewa mutum 5,000 ne suka tafi Masar daga Aljeriya don goyon bayan kungiyar kwallon kafar kasarsu a wasan da za ta yi ranar Juma&#8217;a ya daga hankalin hukumomin Masar din wata kila ma har da hana su barci.<\/p>\n<p>Kasashen biyu manyan abokan adawar juna ne a tarihin kwallon kafa na duniya, kuma an sha samun tashin hankali a fafatawar da ake tsakanin kungiyoyin kasashen biyu a cikin filin wasa ko a wajensa.<\/p>\n<p>Sai dai a wannan karon abubuwa sun sha bambam:<\/p>\n<p>Na farko, tuni aka fitar da kungiyar kwallon kafa ta Masar a gasar cin kofin Afirkar da ake a kasar a zagaye na 16 bayan da Afirka Ta Kudu ta fitar da su a wani lamari da ya zo wa mutane da mamaki.<\/p>\n<p>Fitar da su din ya zama silar kaucewa duk wani tashin hankali da aka yi tunanin zai iya faruwa tsakaninsu da makwabciyar tasu Aljeriya.<\/p>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Iface-iface<\/h2>\n<p>Na biyu, kuma abu mafi ban mamaki: al&#8217;ummar kasar sun yi maraba da &#8216;yan Aljeriyan wadanda ake kira da Kuregun Hamada.<\/p>\n<p>A yayin da Aljeriya ta yi nasara a kan Najeriya 2-1 a wasan kusa da karshe a ranar Litinin, an ga yadda &#8216;yan Masar da dama suka dinga murnar nasarar makwabciyarsu &#8211; kuma ga alama haka za su yi a ranar Juma&#8217;a ma a wasan da za ta buga da Senegal.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTempers have flared up before, during and after past encounters between Egypt and Algeria<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>A takaice dai dukkan magoya bayan kasashen biyu Aljeriya da Masar sun hada kai wajen bujirewa hukumomin Masar a yayin wasan daf da na karshe inda suka dinga ihu tare da kiran sunan wani tsohon dan wasan Masar Mohamed Aboutrika, wanda yake neman mafaka a wata kasar bayan da ya soki mulkin soji karara.<\/p>\n<p>Bayan da aka gama wasan, dan wasan gaba na Aljeriya Youcef Belaili ya ce &#8220;Godiya ga &#8216;yan Masar da suka goya mana baya, Allah ya ji kan shahidanmu.&#8221;<\/p>\n<p>Ba wanda ya taba tunanin irin haka za ta faru. Ko da kuwa an sa batun yanayi da zamantakewa a nahiyar Afirka &#8211; inda Masar da Aljeriya &#8216;yan Afirka ta Arewa ne kuma Larabawa, ba kamar sauran kasashen nahiyar 52 ba.<\/p>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Rigimar da ta wuce<\/h2>\n<p>A tarihi, akwai kyakkyawar alaka tsakanin kasashen biyu &#8211; Masar ta mara wa Aljeriya baya lokacin da take yakin neman &#8216;yancin kanta daga kasar Faransa a shekarun 1954 zuwa 1962.<\/p>\n<p>Sai dai wasannin kwallon kafa kan kare da rikici tsakaninsu a lokuta da dama.<\/p>\n<p>Mafi shahara daga ciki shi ne wanda ya faru a shekarar 1989 a wasan neman cancantar zuwa Kofin Duniya, wanda har ake masa lakabi da &#8220;Yakin Alkahira&#8221; (Battle of Cairo).<\/p>\n<p>Nasarar da Masar da ta yi a wasan ya ba ta damar halartar gasar cin Kofin Duniya na shekarar 1990. Rikicin da ya biyo bayan wasan ya yi sanadiyar makantar da wani jami&#8217;in tawagar kwallon kafar Masar.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTauraron dan wasan Aljeriya Belloumi (daga dama) ya fusaknaci shari&#8217;a ta tsawon lokaci kan &#8220;Yakin Alkahira&#8221;<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Mahukuntan Masar sun zargi Lakhdar Ballouni saboda rikicin, inda aka dauki shekara 20 ana neman kama shi bisa umarnin kotu a kasar.<\/p>\n<p>A shekarar 2009 ma kassashen sun gwabza da juna a wasan cancantar shiga Kofin Duniya. Bayan kowacce ta ci wasan gidanta da 2-0 sai aka ci gaba da buga wasan a birnin Khartoum na Sudan.<\/p>\n<p>An buga wasan ne yayin da shugaban kasar Masar Hosni Mobarak ya yi barazanar tura sojoji domin tsaron lafiyar magoya bayan tawagar kasarsa.<\/p>\n<p>An yi ta zanga-zanga a kasashen biyu, abin da ya kai ga lalata shagunan kasuwancin Masar a kasar Aljeriya.<\/p>\n<p>Aljeriya ce ta lashe wasan da ci 1-0.<\/p>\n<p>Watanni bayan haka, a shekarar 2010 an sallami &#8216;yan wasan Aljeriya uku daga wasan cin Kofin Afirka tsakanin kasashen.<\/p>\n<p>Yayin magoya suka rika fadar maganganu kan Aboutrika a kafafen sada zumnta, ita kuwa hukumar kwallon kafar Afirka ta CAF tana bincike ne kan karawa tsakanin magoya bayan Aljeriya da Masar a wasan kusa da na karshe da Najeriya.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\n&#8216;Yan Aljeriya sujn yi ta murna har a titun birnin Paris na Faransa<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Mahukuntan Masar sun tsaurara tsaro yayin gudanar da gasar musamman kusa da filayen wasanni. Wani mai magana da yawun ma&#8217;aikatar cikin gida ya ce har yanzu ba a samu rahoton rikici ba.<\/p>\n<p>Ya ce: &#8220;&#8216;Yan Aljeriya sun yi murnar nasarar da suka samu tare da &#8216;yan kasar Masar ba tare da wani rikici ba.&#8221;<\/p>\n<p>Wani hoto da wata jaridar Masar Al Ahram ta wallafa a shafinta na Intanet ya nuna wani dan Aljeriya da dan Masar suna murna tare da kuma nuna &#8216;yan uwantaka.<\/p>\n<p>Wani dan Masar Mohammed Mosen ya ce: &#8220;Mun yi abota da su kuma mun koyi wakokinsu har ma muka rika rera shahararren takensu na &#8216;1, 2, 3 vive l&#8217;Alg\u00e9rie,&#8217; kuma sun ji dadin yadda muka goyi bayansu.<\/p>\n<p>Mun yi imamnin cewa sun cancanci mu goyi bayansu saboda su ne kan gaba zuwa yanzu a filin kwallo da kuma kokarinsu.&#8221;<\/p>\n<p>Sai dai abu ne a boye ko wannan &#8216;yan uwantakar za ta dore har zuwa karshen wasan.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Image caption Shin &#8216;yan Aljeriya da Masar sun warware rashin jituwar da ke tsakaninsu a fagen kwallon kafa? &#8212;BBC Hausa Labarin cewa mutum 5,000 ne suka tafi Masar daga Aljeriya don goyon bayan kungiyar kwallon kafar kasarsu a wasan da za ta yi ranar Juma&#8217;a ya daga hankalin hukumomin Masar [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":136850,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[9688,12784,128],"class_list":["post-136849","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-afcon","tag-algeriya","tag-egypt"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/136849","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=136849"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/136849\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/136850"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=136849"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=136849"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=136849"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}