{"id":135836,"date":"2019-07-15T07:54:58","date_gmt":"2019-07-15T06:54:58","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=135836"},"modified":"2019-07-15T07:55:20","modified_gmt":"2019-07-15T06:55:20","slug":"satar-mutane-akwai-jan-aiki-gaban-gwamnatin-najeriya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=135836","title":{"rendered":"Satar mutane: Akwai jan aiki gaban gwamnatin Najeriya"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"BBC\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/07\/Satar-mutane-Akwai-jan-aiki-gaban-gwamnatin-Najeriya.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">A yayin da ake tunanin cewa an fara samun sa&#8217;ida da kuma sauki game da satar mutane domin neman kudin fansa a wasu jihohi na arewa-maso-yammacin Najeriya, wasu na ci gaba da kokakawa kan irin matsalolin da ake samu na garkuwa da mutane.<\/p>\n<p>Jama&#8217;ar da ke iyaka da jihohin Kaduna da Zamfara da kuma Neja na kukan cewa an bar irin wadannan &#8216;yan bindiga suna cin karensu babu babbaka a dajin da ke yankin.<\/p>\n<p>Ko a yammacin Asabar sai da wasu mahara suka shiga kauyen Kurebe da ke karamar hukumar Shiroro na jihar Neja, inda suka harbi mutum biyu da yin awon-gaba da shanu masu dinbin yawa.<\/p>\n<p>Sai dai wani matashi da ya samu tsira bayan ya kwashe sama da kwana arba&#8217;in a hannun masu satar mutane, wanda ya ce yanzu haka ya koma wani na daban inda yake neman aikin da zai yi saboda tashin hankalin da yankin na su ke ciki a kullu-yaumin, ya ce abin kara kamari yake yi a dajin da ke tsakanin wadannan jihohi uku.<\/p>\n<p>Ganin cewa matashin ya dade hannun &#8216;yan bindigar kuma ya ga yadda suke cin karensu babu babbaka, ya shaida wa BBC cewa bai bayan irin abubuwan da ya gani a wannan wuri, bai yi tsammanin matakan da jami&#8217;an tsaro ke dauka a yanzu ba ko za su magance wannan lamarin.<\/p>\n<p>Ya bayyana cewa har yanzu akwai wasu kauyukan da &#8216;yan bindigar ke masu barazana inda suke cewa sai sun bayar da kudi kafin su bar su su noma gonakinsu.<\/p>\n<p>Batun garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa matsala ce da ta dade tana ci wa &#8216;yan Najeriya tuwo a kwarya musamman a jihohin arewa mmaso yammacin kasar.<\/p>\n<p>Sai dai da alamu duk da tashi tsaye da wasu gwamnatocin jihohi suka yi domin kawo karshen lamarin, har yanzu hakarsu bata cimma ruwa ba.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>A yayin da ake tunanin cewa an fara samun sa&#8217;ida da kuma sauki game da satar mutane domin neman kudin fansa a wasu jihohi na arewa-maso-yammacin Najeriya, wasu na ci gaba da kokakawa kan irin matsalolin da ake samu na garkuwa da mutane. Jama&#8217;ar da ke iyaka da jihohin Kaduna da Zamfara da kuma Neja [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":135837,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[12748],"class_list":["post-135836","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-garkuwa-da-mutane"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/135836","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=135836"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/135836\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/135837"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=135836"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=135836"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=135836"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}