{"id":133002,"date":"2019-07-05T07:55:43","date_gmt":"2019-07-05T06:55:43","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=133002"},"modified":"2019-07-05T07:56:13","modified_gmt":"2019-07-05T06:56:13","slug":"yaushe-kotu-za-ta-yanke-hukunci-kan-zaben-gwamnan-kano-bbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=133002","title":{"rendered":"Yaushe kotu za ta yanke hukunci kan zaben gwamnan Kano? | BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Abba Kabir Yusuf\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/07\/Yaushe-kotu-za-ta-yanke-hukunci-kan-zaben-gwamnan-Kano.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nAbba Kabir Yusuf yana kalubalantar nasarar Gwamna Ganduje<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">A ranar Alhamis ne kotun mai sauraron kararrakin zaben gwamna ta fara zaman share-fage a kan karar da ke gabanta.<\/p>\n<p>Abba Yusuf, wanda aka fi sani da &#8220;Abba gida-gida&#8221;, ya sha kayi a hannun Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a karashen zaben da aka yi, duk da cewa shi ne kan gaba a zaben farko wanda bai kammala ba.<\/p>\n<p>Sai dai masu sa ido na gida da waje sun soki yadda aka gudanar da karashen zaben suna masu cewa an tafka magudi, zargin da jam&#8217;iyyar APC da kuma hukumar zabe suka musanta.<\/p>\n<p>Kotun dai tana da kwana 180 ne ta yanke hukunci daga ranar da aka shigar da karar. A ranar 11 ga watan Afrilun 2019 ne Abba ya shigar da karar.<\/p>\n<p>Ke nan kwanaki 97 ya rage ita wannan kotu ta kammala shari&#8217;ar domin yanke hukunci.<\/p>\n<p>Zaman kotun na ranar Alhamis wanda mai shari&#8217;a Halima Shamaki ke jagoranta, ya mayar da hankali ne kan tantance bayanai da korafe-korafen da bangaren masu kara da na masu kare kai suka gabatar.<\/p>\n<p>An dai tabka muhawara a tsakanin lauyoyin, inda kowane bangare ya nemi da a kori karar da daya bangaren ya shigar kafin daga bisani kotu ta cimma matsayar dage zaman.<\/p>\n<p>Lauyoyin da ke kare Gwamna Ganduje sun nemi a dage sauraron karar, tare da ba su isasshen lokaci domin su yi nazarin wata sabuwar bukatar da masu kara suka gabatar.<\/p>\n<p>Su ma masu gabatar da karar sun ki amincewa da ita, sakamakon zargin da suke yi cewa lauyoyin da ke kariya na fitar da salo ne kawai na ba ta lokaci.<\/p>\n<p>Dan takarar gwamna na jam`iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf da kuma jam`iyyarsa ne suka shigar da karar bisa zargin cewa zaben cike yake da magudi da kuma aika-aikar `yan bangar siyasa.<\/p>\n<p>Haka kuma masu karar sun bukaci kotu ta yi watsi da sakamakon zaben da aka yi, zagaye na biyu, wanda aka fi sani da &#8220;Inconclusive,&#8221; bisa zargin cewa babu tsarin Inconclusive a cikin dokar zabe.<\/p>\n<p>Abba Kabir Yusuf da kuma jam`iyyarsa na karar Hukumar Zabe ta Kasa, INEC da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne, amma sun musanta zarge-zargen na PDP.<\/p>\n<p>Yanzu dai kotun ta dage zaman sauraron karar zuwa ranar 13 ga wannan watan na Yuli, don ci gaba da shari&#8217;ar.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\"><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nHukumar zabe ta bayyana Gwamna Ganduje da wanda ya lashe zaben da aka yi a watan Maris<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<ul class=\"story-body__unordered-list\">\n<li class=\"story-body__list-item\">Kawunan masana shari&#8217;a ya rabu kan zaben Kano<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Duk wanda ya ci zaben Kano a ba shi kawai &#8211; Bashir Tofa<\/li>\n<\/ul>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Yaushe za a kammala shari&#8217;ar?<\/h2>\n<p>Barrister Audu Bulama Bukarti ya yi wa BBC bayanin abubuwan da za su faru daga ranar 13 ga watan Yuli idan kotu ta koma zamanta kamar haka:<\/p>\n<ul class=\"story-body__unordered-list\">\n<li class=\"story-body__list-item\">Masu kara za su gabatar da shaidunsu<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Daga nan kuma sai a bai wa wadanda ake kara su ma su gabatar da nasu shaidun<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Kotun za ta saurari abin da ake kira jawaban karshe, inda wadanda ake kara za su fara jawabin karshen<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Daga nan ne kuma sai a bai wa bangaren masu kara su gabatar da nasu jawabin na karshe<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Kotun za ta sake bai wa wadanda ake kara damar mayar da martani kan jawabin karshe da masu kara suka yi<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Bayan sauraron jawaban karshe da martani sai kotu ta sa ranar yanke hukunci.<\/li>\n<\/ul>\n<p><strong>Daya daga cikin hukunci<\/strong><strong> uku da kotu za ta <\/strong><strong>iya <\/strong><strong>yanke<\/strong><strong>wa<\/strong><\/p>\n<ul class=\"story-body__unordered-list\">\n<li class=\"story-body__list-item\">Kotu za ta iya korar karar da Abba Kabir Yusuf, inda za ta tabbatar da Gwamna Ganduje da cin zabe<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Kotu za ta iya ayyana Abba Kabir Yusuf da wanda ya ci zabe<\/li>\n<li class=\"story-body__list-item\">Kotun za ta iya soke zaben domin a sake<\/li>\n<\/ul>\n<p>Idan hukuncin da kotun sauraron kararrakin zaben ta yanke bai gamsar da daya daga cikin bangarorin ba, sai su garzaya kotun daukaka kara.<\/p>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Yaushe za a yanke hukunci?<\/h2>\n<p>Ita dai wannan kotun ta sauraron kararrakin zaben na da kwanaki 180 ta yanke hukunci daga ranar da aka shigar da karar.<\/p>\n<p>Kotun Daukaka Kara na da kwana 60 ta yanke hukunci, inda ita ma Kotun Koli take da kwanakin 60 ta yanke nata hukuncin.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Image caption Abba Kabir Yusuf yana kalubalantar nasarar Gwamna Ganduje A ranar Alhamis ne kotun mai sauraron kararrakin zaben gwamna ta fara zaman share-fage a kan karar da ke gabanta. Abba Yusuf, wanda aka fi sani da &#8220;Abba gida-gida&#8221;, ya sha kayi a hannun Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a karashen zaben da aka yi, duk [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":133003,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[12641,3446,11178],"class_list":["post-133002","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-abba-gida-gida","tag-ganduje","tag-kano-guber"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/133002","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=133002"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/133002\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/133003"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=133002"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=133002"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=133002"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}