{"id":132672,"date":"2019-07-04T16:28:21","date_gmt":"2019-07-04T15:28:21","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=132672"},"modified":"2019-07-04T16:28:46","modified_gmt":"2019-07-04T15:28:46","slug":"ba-halina-ba-ne-ku-yafe-min-sanata-abbo-bbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=132672","title":{"rendered":"Ba halina ba ne ku yafe min &#8211; Sanata Abbo | BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Senator Elisha Abbo win election on February 23, 2019 as Senator representing senatorial senatorial district\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/07\/Yan-sanda-sun-fara-binciken-Sanata-Elisha-Abbo.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><br \/>\n<span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Elisha Abbo<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nSanata Elisha Abbo na jam&#8217;iyyar PDP yana wakiltar shiyyar arewacin jihar Adamawa ne<\/span><\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Dan majalisar dattijan wanda bayanai suka ambato shi cike da nadama a taron manema labaran da ya yi cikin shalkwatar jam&#8217;iyyarsa ta PDP da ke Abuja, ya nemi gafara, kuma ya ce a yafe masa.<\/p>\n<p>Sanata Elisha Abbo, wanda ke wakiltar shiyyar arewacin jihar Adamawa, ya ce &#8220;ba halina ba ne tozarta mata, don haka na yi nadama&#8221;.<\/p>\n<p>Faifan bidiyon dai ya tayar da kura da kuma janyo tofin Allah-tsine daga masu fafutuka da dumbin &#8216;yan Najeriya har ma da fitattun &#8216;yan siyasa musamman a shafukan sada zumunta.<\/p>\n<p>Rundunar &#8216;yan sandan Najeriya ta ce ta fara gudanar da bincike kan zargin cin zarafin matar.<\/p>\n<p>Lamarin ya faru ne a wani shagon sayar da kayan wasannin jima&#8217;i da sanatan ya ziyarta tare da rakiyar wasu mata.<\/p>\n<p>A taron manema labaran da ya yi, Sanata Abbo ya ce &#8220;Ba na zo nan ba ne don yin bayani kan abin da ya faru ta bangarena. Na zo ne don neman afuwar &#8216;yan Najeriya saboda bata musu rayukan da na yi.&#8221;<\/p>\n<p>&#8220;Cikin matukar nadama da sanin ciwon kai, ni Ishaku Abbo nake matukar neman gafarar duk &#8216;yan Najeriya da majalisar dattijai da jam&#8217;iyyar PDP da iyalina da abokaina da kuma uwayenmu, matan Najeriya.<\/p>\n<p>Ni da kaina kuma ina neman afuwar Bibra[wacce ya ci zarafi], da danginta saboda abin da na yi. Duk ma dai abin da kika yi mini, ba ki cancanci irin wannan mataki ba, ki yi hakuri!&#8221; In ji Matashin sanatan mai shekara 41.<\/p>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Ya kamata PDP ta dauki mataki a kansa<\/h2>\n<p>Bidiyon dan majalisar a shagon sayar da kayan wasannin jima&#8217;i da ke ikirarin nuna shi yana dukan mai tsaron kanti, ya janyo fushi da bacin rayuka.<\/p>\n<p>Mutane da dama ciki har da dan takarar shugaban kasa na baya-bayan nan a jam&#8217;iyyar PDP Atiku Abubakar suka bukaci a gurfanar da shi gaban hukunci tare da neman majalisar dattijai ta koya masa ladabi.<\/p>\n<p>A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Atiku ya ce kamata jam&#8217;iyyar PDP ta dauki matakin ladaftarwa a kan sanatan.<\/p>\n<p>&#8220;Ina shawartarsa da ya fito fili ya nemi afuwa sannan ya mika kansa ga &#8216;yan sanda domin ya nuna dattako.<\/p>\n<p>&#8220;Sannan kuma ina kira ga uwar jam&#8217;iyyarmu ta PDP da ta dauki matakin ladaftarwa a kansa, su ma &#8216;yan sanda su tabbatar cewa doka ta yi aikinta.&#8221;<\/p>\n<p>Afuwar da sanatan ya nema ta zo ne sa&#8217;o&#8217;i kadan bayan kiran da Atiku Abubakar ya yi masa na ya yi hakan.<\/p>\n<p>Rundunar &#8216;yan sandan kasar ta alkawarta sanar da &#8216;yan Najeriya sakamakon bincike da ta fara gudanarwa.<\/p>\n<p>Ita ma majalisar dattijan kasar ta kafa kwamiti domin ya binciki wannan batu a daidai lokacin da jam&#8217;iyyarsa ta PDP ta fito ta yi Alla-wadai da halayyar cin zarafin da ake zargin sanatan ya yi wa wannan mata mai shayarwa.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Elisha Abbo Image caption Sanata Elisha Abbo na jam&#8217;iyyar PDP yana wakiltar shiyyar arewacin jihar Adamawa ne Dan majalisar dattijan wanda bayanai suka ambato shi cike da nadama a taron manema labaran da ya yi cikin shalkwatar jam&#8217;iyyarsa ta PDP da ke Abuja, ya nemi gafara, kuma ya ce a yafe masa. [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":132458,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[11530,12633],"class_list":["post-132672","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-bbc-hausa","tag-sanata-abbo"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/132672","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=132672"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/132672\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/132458"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=132672"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=132672"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=132672"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}