{"id":127075,"date":"2019-06-16T11:00:00","date_gmt":"2019-06-16T10:00:00","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=127075"},"modified":"2019-06-16T11:02:15","modified_gmt":"2019-06-16T10:02:15","slug":"an-sake-kashe-mutane-da-dama-a-harin-zamfara","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=127075","title":{"rendered":"An sake kashe mutane da dama a harin Zamfara"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Matawalle\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/06\/Rikicin-jihar-Zamfara-ya-fara-yin-awon-gaba-da-masu-sarauta.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><figcaption class=\"media-caption\"><span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nGwamna Matawalle ya sha alwashin magance matsalar tsaro a Zamfara<\/span><\/p>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Rundunar &#8216;yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da cewa an kashe mutum 34 a wani hari da &#8216;yan fashin daji suka kai kan kauyen Tungar Kahau cikin karamar hukumar Shinkafi.<\/p>\n<p>Sai dai wasu mazaunan yankin Shinkafi sun ce mutanen da aka kashe sun kai 42, inda a ranar da aka kai harin aka samu gawawwakin mutum 40, kafin washe gari kuma a gano karin gawa biyu.<\/p>\n<p>Wannan shi ne na baya-bayan nan cikin hare-haren &#8216;yan fashin daji wadanda suka addabi jihar Zamfara, da ma karin wasu jihohi da ke makwabtaka da ita.<\/p>\n<p>Kwanan baya ma sai da aka kai hari kan kauyen Kanoma inda aka kashe mutane, lamarin da daga bisani ya janyo dakatar da wani babban basarake da kuma hakimin yankin.<\/p>\n<p>Bayanai dai sun ce tuni mutanen Tungar Kahau suka tsere zuwa manyan garuruwa da ke ciki da wajen jihar Zamfara bayan harin ranar yammacin Juma&#8217;a.<\/p>\n<p>&#8220;Gaskiyar magana, kauyen gaba daya ya watse, mutane duk inda ka duba kowa kuka kawai yake ta yi&#8230;kowa dar-dar yake yi kada dare ya yi masa a wannan kauye&#8221; in ji wani shaida.<\/p>\n<p>Haka zalika wani da ya tsira daga harin ya shaida wa BBC cewa da yamma ne kwatsam maharan suka auka musu da harbin kan mai-uwa-da-wabi.<\/p>\n<p>Ya ce da kyar Allah ya kubutar da shi tare da wani abokinsa, inda suka tsere zuwa garin Shinkafi, a cewarsa da dama ba su san inda dangin da &#8216;yan&#8217;uwansu suka shiga ba, bayan maharan sun kutsa kai cikin kauye.<\/p>\n<p>Mai magana da yawun rundunar, Muhammed Shehu ya fada wa wakilinmu Sani Aliyu cewa tuni aka tura karin jami&#8217;an tsaro da suka je yankin don farautar maharan a cikin daji.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Gwamna Matawalle ya sha alwashin magance matsalar tsaro a Zamfara Rundunar &#8216;yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da cewa an kashe mutum 34 a wani hari da &#8216;yan fashin daji suka kai kan kauyen Tungar Kahau cikin karamar hukumar Shinkafi. Sai dai wasu mazaunan yankin Shinkafi sun ce mutanen da aka kashe sun kai 42, [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":124153,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[],"class_list":["post-127075","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/127075","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=127075"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/127075\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/124153"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=127075"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=127075"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=127075"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}