{"id":123999,"date":"2019-06-06T06:58:28","date_gmt":"2019-06-06T05:58:28","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=123999"},"modified":"2019-06-06T06:58:43","modified_gmt":"2019-06-06T05:58:43","slug":"an-kwace-kofin-zakarun-afirka-bbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=123999","title":{"rendered":"An kwace kofin Zakarun Afirka | BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"'Yan wasan Esperance da kofin Zakarun Afirka\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/06\/An-kwace-kofin-Zakarun-Afirka.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Reuters<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nDa farko an ba wa &#8216;yan Esperance nasara, aka mika musu kofin, to amma yanzu sai sun sake wasan karo na biyu<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">An umarci &#8216;yan kwallon kafar kungiyar Esperance ta Tunisiya da su mayar da kofin Zakarun Afirka da suka ci a makon da ya gabata, domin a sake wasa.<\/p>\n<p>Hukumar kwallon kafa ta Afirka, CAF, ta yanke hukuncin cewa dole ne kungiyar ta sake maimaita wasanta na karshe na biyu, da Wydad Casablanca.<\/p>\n<p>A fafatawarsu ta biyu a Tunisiya, &#8216;yan wasan kungiyar ta Moroko sun ki yarda su ci gaba da wasa har aka tashi saboda wata takaddama kan kwallon da suka ci aka hana.<\/p>\n<p>Ita dai kungiyar Esperance ta Tunisiya ta yi canjaras ne a wasan karshen na karon farko da abokiyar karawar tata, Wydad Casablanca a can Moroko.<\/p>\n<p>A karawarsu ta biyu ne a Tunisiya, Esperance din tana gaba a wasan da ci daya ba ko daya, sai bakin, &#8216;yan Wydad suka farke kwallon, to amma alkalin wasa ya hana.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption body-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Others<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTakaddama kan kwallon da &#8216;yan Wydad suka rama, lafiri ya hana<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Wannan ne ya sa &#8216;yan kungiyar ta Moroko suka bukaci da lafirin da ya je ya duba na&#8217;urar hoton bidiyon da ke taimakawa wajen warware takaddama, domin, sanin gaskiyar lamarin.<\/p>\n<p>To sai dai daga nan ne aka ce musu wannan na&#8217;ura ta VAR, da ke gefen fili, ba ta aiki, a kan hakan su kuma suka ce atafau, ba za su ci gaba da wasan ba.<\/p>\n<p>Hakan ne kuma ya sa hukumomin wasan suka ayyana Esperance a matsayin wadda ta ci kofin na Zakarun Afirka, aka ba ta kofin.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">AFP<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nTun da farko ba a gaya wa &#8216;yan wasan na&#8217;urar VAR din ba ta aiki ba<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Bayan nazari kan batun ne, a yanzu hukumar kwallon kafa ta Afirka ta bayar da umarnin a sake wasan, wannan karon kuma a wata kasa &#8216;yar ba-ruwanmu.<\/p>\n<p>Sai dai kasancewar a yanzu ana dab da fara gasar cin kofin kwallon kafa na kasashen Afirka, ba za a sake wannan wasa na karshe ba, har sai a karshen watan Yuli.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Reuters Image caption Da farko an ba wa &#8216;yan Esperance nasara, aka mika musu kofin, to amma yanzu sai sun sake wasan karo na biyu An umarci &#8216;yan kwallon kafar kungiyar Esperance ta Tunisiya da su mayar da kofin Zakarun Afirka da suka ci a makon da ya gabata, domin a sake [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":124000,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[11509],"class_list":["post-123999","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-2019-afcon"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/123999","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=123999"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/123999\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/124000"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=123999"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=123999"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=123999"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}