{"id":123743,"date":"2019-06-05T06:43:55","date_gmt":"2019-06-05T05:43:55","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=123743"},"modified":"2019-06-05T06:50:11","modified_gmt":"2019-06-05T05:50:11","slug":"rashin-aiki-ya-zama-balai-na-kasa-bbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=123743","title":{"rendered":"Rashin aiki ya zama bala&#8217;i na kasa | BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"wasta mata a Afirka ta Kudu na shanya\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/06\/Rashin-aiki-ya-zama-balai-na-kasa.jpg\" width=\"976\" height=\"549\" data-temp-aztec-id=\"c840ebd4-7636-47c4-9c1a-b8731bb09875\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nFatara da rashin aikin yi sun fi wanzuwa a tsakanin bakar fata a kasar ta Afirka ta Kudu<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Jam&#8217;iyyar ANC mai mulki a Afirka ta Kudu ta ce arzikin cikin gida na kasa ya ragu da kashi 3.2 cikin dari a wata ukun farko na wannan shekara idan aka kwatanta da shekaru uku na karshen shekarar da ta gabata.<\/p>\n<p>Babban Sakataren jam&#8217;iyyar, Ace Magashule ya ce wannan shi ne koma-baya mafi muni a cikin shekara goma, a kasar ta Afirka ta Kudu.<\/p>\n<p>Sakatare Janar din yana bayani ne a wani taron manema labarai a wurin taron kwamitin zartarwa na jam&#8217;iyyar a karshen mako.<\/p>\n<p>Shi dai wannan taro, zama ne da yake hado kan &#8216;yan kwamitin zartarwa na jam&#8217;iyyar ANC hadi da &#8216;yan kungiyoyin da ta yi hadaka da su na kwadago tare kuma da &#8216;yan majalisar dokokin kasar nata.<\/p>\n<p>Sakatare Janar din na ANC, ya gaya wa manema labaran a hedikwatar jam&#8217;iyyar a birnin Johannesburg cewa, &#8216;sun kaddamar da matsalar rashin aikin yi a matsayin bala&#8217;i na kasa.<\/p>\n<p>Sannan ya ce jam&#8217;iyyar mai mulki za ta bunkasa tattalin arzikin kasar ta yadda zai amfani dukkanin &#8216;yan Afirka ta Kudu da kuma samar da ayyukan yi.<\/p>\n<p>Wannan dai shi ne taro irinsa na farko tun bayan da jam&#8217;iyyar ta yi nasara a babban zaben kasar a watan da ya gabata, inda ta samu kashi 57 cikin dari na kuri&#8217;u.<\/p>\n<p>Jami&#8217;in ya ce wani karin dalili na yin wannan taron shi ne domin nazari a kan dumokuradiyyar kasar ta shekara 25 da kuma tsara yadda za su aiwatar da manufofinsu na neman samar da tartibin shiri na shekara biyar, don ciyar da kasar gaba.<\/p>\n<p>Jam&#8217;iyyar ta ANC ta duba nasarar da ta yi tun lokacin da ta hau mulki a shekara ta 1994, inda ta ce tattalin arzikin kasar ya burunkasa bayan gomman shekaru na koma-baya a karkashin mulkin tsiraru farar fata.<\/p>\n<p>Sannan ta ce arzikin kasar ya linka har sau uku kuma aikin yi ya linka biyu a tsawon wannan lokaci na mulkin da take yi tun bayan karbe ragamar iko daga mulkin wariyar launin fata.<\/p>\n<p>Jam&#8217;iyyar wadda ta taso da fafutukar &#8216;yanto bakar fatar kasar tsawon shekara 107, ta ce, duk da wannan ci-gaba wanzuwar fatara da rashin aikin yi da rashin daidaito musamman a dalilai na wariyar launin fata da bambanci tsakanin maza da mata sun ci gaba da kasancewa.<\/p>\n<p>Sai dai ANC din ba ta ambaci illar cin hanci da rashawa ba da aka samu a kasar ta Afirka ta Kudu, karkashin mulkinta.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Image caption Fatara da rashin aikin yi sun fi wanzuwa a tsakanin bakar fata a kasar ta Afirka ta Kudu Jam&#8217;iyyar ANC mai mulki a Afirka ta Kudu ta ce arzikin cikin gida na kasa ya ragu da kashi 3.2 cikin dari a wata ukun farko na wannan shekara idan [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":123744,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681,4],"tags":[8292,354],"class_list":["post-123743","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","category-politics","tag-cyril-ramaphosa","tag-south-africa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/123743","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=123743"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/123743\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/123744"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=123743"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=123743"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=123743"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}