{"id":115247,"date":"2019-05-09T07:18:10","date_gmt":"2019-05-09T06:18:10","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=115247"},"modified":"2019-05-09T07:21:13","modified_gmt":"2019-05-09T06:21:13","slug":"an-gama-kada-kuria-a-babban-zaben-afirka-ta-kudu","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=115247","title":{"rendered":"An gama kada kuri&#8217;a a babban zaben Afirka ta Kudu"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Shugaba Cyril Ramaphosa\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/05\/An-kammala-kada-kuria-a-babban-zaben-Afirka-ta-Kudu.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">MICHELE SPATARI<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nShugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu<\/span><\/p>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">&#8216;Yan Afirka ta Kudu sun fito kwansu da kwarkwatarsu daga birane zuwa kauyuka domin zaben wadanda za su jagorance su nan da shekaru biyar masu zuwa.<\/p>\n<p>A lokacin da ya kada kuri&#8217;arsa, Shugaba Cyril Ramaphosa ya bai wa &#8216;yan kasar hakuri saboda abin da ya kira &#8216;kuskuren da jam&#8217;iyyarsa ta ANC ta yi a shekarun da ta shafe tana mulkin kasar.<\/p>\n<p>Amma shugaban ya ce yana da karfin gwuiwa cewa jamiiyyar tasa za ta sami nasara kuma yayi alkawarin kawo sauyi mai ma&#8217;ana da zarar hakan ya samu.<\/p>\n<p>Masu nazarin harkokin siyasar kasar na ganin wannan zaben zai kasance wanda ya fi jan hankulan &#8216;yan kasar, kuma za a fafata sosai tsakanin manyan jam&#8217;iyyun siyasa na kasar.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Reuters<\/span><figcaption class=\"media-caption\">\n<span class=\"off-screen\">Image caption<\/span><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nMasu kada kuri&#8217;a sun tsaya kan layi har dare a wasu yankunan kasar<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p>Mutane da dama sun ce za su mara wa jam&#8217;iyyar ANC mai mulkin kasar baya&#8230; inda suke fatan Shugaba Cyril Ramaphosa zai kawo karshen shekaru goma na koma bayan tattalin arziki da rashin iya mulki a kasar.<\/p>\n<p>A yayin da ya ke kada tasa kuri&#8217;ar a wata rumfar zabe, Mista Ramaphosa ya ba al&#8217;umomin kasar hakuri kan abin da ya kira matsalar cin hanci da rashawar da suka ki ci, suka ki cinyewa.<\/p>\n<p>Jagoran jam&#8217;iyyar adawa ta Democratic Alliance, Mmusi Maimane ya yi kira ga jama&#8217;ar kasar da su mara wa jam&#8217;iyyarsa baya, kuma su kawo sauyi na siyasa mai ma&#8217;ana a kasar.<\/p>\n<p>Duk da cewa ANC ce ake sa ran za ta lashe zaben a matakin tarayya, amma za ta sha kaye a wasu larduna na kasar masu muhimmanci matuka.<\/p>\n<p>Ita ma jam&#8217;iyyar Economic Freedom Fighters, EFF za ta kara karfi, kuma za ta iya zama wata muhimmiyar jam&#8217;iyyar siyasa a kasar.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto MICHELE SPATARI Image caption Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu &#8216;Yan Afirka ta Kudu sun fito kwansu da kwarkwatarsu daga birane zuwa kauyuka domin zaben wadanda za su jagorance su nan da shekaru biyar masu zuwa. A lokacin da ya kada kuri&#8217;arsa, Shugaba Cyril Ramaphosa ya bai wa &#8216;yan kasar hakuri [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":115248,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[8292,354,11938],"class_list":["post-115247","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-cyril-ramaphosa","tag-south-africa","tag-zuma"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/115247","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=115247"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/115247\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/115248"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=115247"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=115247"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=115247"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}