{"id":109219,"date":"2019-04-20T17:51:19","date_gmt":"2019-04-20T16:51:19","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=109219"},"modified":"2019-04-20T17:51:46","modified_gmt":"2019-04-20T16:51:46","slug":"me-ke-hana-yan-wasan-najeriya-dadewa-suna-haskawabbc-hausa","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=109219","title":{"rendered":"Me ke hana &#8216;yan wasan Najeriya dadewa suna haskawa?|BBC Hausa"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Taye Taiwo da Lionel Messi\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/04\/Me-ke-hana-yan-wasan-Najeriya-dadewa-suna-haskawa.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<ul class=\"story-body__unordered-list\">\n<li class=\"story-body__list-item\"><i>Wannan makala ce da wani mai sharhi kan harkokin wasanni a Najeriya Isiyaku Muhammad <\/i><i>Ango <\/i><i>ya rubuta mana<\/i><i>.<\/i><\/li>\n<\/ul>\n<p class=\"story-body__introduction\">A duk lokacin da ake batun &#8216;yan wasan kwallon kafa a duniya, zai yi wuya a shafa fatiha ba tare da an kira Najeriya ba saboda yadda kasar ke fitar da zaratan &#8216;yan wasa da suke tasiri a duniya.<\/p>\n<p>&#8216;Yan wasan Najeriya da dama sukan fito da karfinsu, amma abin mamaki cikin kankanin lokaci sai ka neme su ka rasa, abin kamar almara.<\/p>\n<p>Idan an je gasar cin kofin &#8216;yan kasa da shekara 17 da 20, har kasar Brazil da ake ganin ta shahara a kwallon kafa, ta kan yi fargaba haduwa da Najeriya.<\/p>\n<p>Misali a gasar cin Kofin Duniya na &#8216;yan kasa da shekara 17 wato U-17, Najeriya ta fi kowace kasa lashe gasar, inda ta ci kofin sau biyar a shekarun 1985 da 1993 da 2007 da 2013 da 2015, sannan kuma ta zo na biyu a shekarun 1987 da 2001 da 2009.<\/p>\n<p>Sai kasar Brazil wadda ta lashe gasar sau uku.<\/p>\n<p>Kuma Najeriya ta kan samu kyaututtuka kamar ta dan wasan da ya fi zura kwallaye (Golden Boot) da sauransu.<\/p>\n<p>Haka gasar &#8216;yan kasa da shekara 20 wanda duk da ba ta taba lashewa ba, Najeriya ta zo ta biyu sau biyu a shekarun 1989 da 2005.<\/p>\n<p>Amma yawancin lokuta, &#8216;yan wasan kasashen wajen sai tauraronsu ya ci gaba da haskawa, amma &#8216;yan Najeriya kuma ta su ta rika dusashewa.<\/p>\n<p>Misalan &#8216;yan wasan Najeriya da takwarorinsu na kasashen waje da suka taso tare:<\/p>\n<p><strong>1. Crisantus Macauley da Toni Kroos da Eden Hazard da David De Gea<\/strong><\/p>\n<p>A gasar cin Kofin Duniya ta &#8216;yan kasa da shekara 17 a shekarar 2007 da aka buga a kasar Koriya ta Kudu.<\/p>\n<p>Najeriya ce ta lashe gasar, sannan kuma dan kasar Crisantus Macauley ne ya fi zuwa kwallaye (Golden Boot), sannan kuma ya zo na biyu a wadanda suka fi iya taka leda (Silver Ball) bayan Toni Kross (Golden Ball) sannan Bojan Krkic na uku wanda yanzu yake Stoke City a Ingila.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>Yanzu haka Crisantus yana kulob din UB Conquense da ke rukunin Tercera na Spain.<\/p>\n<p>Tercera ne rukuni na hudu a Spain bayan Laliga da Segunda da Segunda B.<\/p>\n<p>Amma Kroos yanzu haka ana iya cewa ya ci komai a duniyar kwallo kamar Gasar Zakarun Turai sau hudu da Kofin Duniya da La liga da Bundesliga sau uku da sauransu.<\/p>\n<p>Sauran &#8216;yan wasan gasar akwai Bojan da Daniel Welbeck da Victor Moses (lokacin yana wakiltar Ingila) da Cristian Benteke da Nacho.<\/p>\n<p>Amma duk da wadannan &#8216;yan wasan, Crisantus ne ya lashe kyautar Golden Ball da Silver Boot.<\/p>\n<p><strong>2. Mikel Obi da Taye Taiwo da Lionel Messi<\/strong><\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Facebook<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>A gasar cin Kofin Duniya na &#8216;yan kasa da shekara 20 ta shekarar 2005 a Holland lokacin ana kiran gasar World Youth Championship, inda Ajantina ta lallasa Najeriya da ci biyu da nema a wasan karshe.<\/p>\n<p>Mikel Obi ne na biyu a cikin wadanda suka fi taka leda a gasar (Silver Boot) bayan Messi da ya zo na daya (Golden Boot).<\/p>\n<p>Yanzu Mikel yana kungiyar Middlesbrough ne ta rukuni na biyu a Ingila, shi kuma Messi abin ba a cewa komai.<\/p>\n<p>Sai kuma Taye Taiwo, wanda shi kuma yanzu haka yake rara-gefe a kasar Finland a kungiyar RoPS.<\/p>\n<p>Sauran &#8216;yan wasan da suka buga gasar sun hada da Fagregas da Aguero da sauransu.<\/p>\n<p><strong>3. Sani Emmaneul, Abdul Ajagun, Neymar Jnr, Isco, da Morata<\/strong><\/p>\n<p>A gasar Kofin Duniya ta 2009 a Najeriya inda kasar Switzerland ta doke Najeriya a bugun karshe.<\/p>\n<p>Dan wasan Najeriya Sani Emmanuel ne ya lashe kyautar wanda ya fi taka leda (Golden Boot).<\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\">\n<p><span class=\"off-screen\">Hakkin mallakar hoto<\/span><br \/>\n<span class=\"story-image-copyright\">Getty Images<\/span><\/p>\n<\/figure>\n<p>Amma tun a shekarar 2015 da ya bar Oskarshamn a Sweden, har yanzu yana zaman kashe wando ne.<\/p>\n<p>Shi kuma Ajagun, wanda a lokacin shi ne kyaftin yana kungiyar Omonia Nikosia a kasar Cyprus a matsayin aro daga KV Kortrijk ta Holland.<\/p>\n<p>Sauran &#8216;yan wasan gasar sun hada da Marc-Andre ter Stegen &#8211; wato golan Barcelona, da Mario Gotze da Kenneth Omeruo na Najeriya da Coutinho da Casemiro da sauransu.<\/p>\n<p>Amma duk da wadannan &#8216;yan wasan, dan Najeriya ne ya lashe kyautar Golden Boot.<\/p>\n<p>Sauran &#8216;yan wasa da suka taso amma suka yi kasa daga baya akwai Kellechi Iheanacho (Leicester City) da Musa Yahaya (FC Porto B) da sauransu.<\/p>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Dalilin da tauraronsu ke dusashewa da sauri<\/h2>\n<p>Akwai abubuwa da suke taimakawa wajen dusashen haske da tauraron &#8216;yan wasan Najeriya cikin sauri. Amma manyan abubuwan sun hada da:<\/p>\n<p><strong>1. Talauci.<\/strong><\/p>\n<p>Da yawa daga cikin masu kallon kwallo za su yi mamaki ganin talauci a matsayin abin da ke jawo wa &#8216;yan wasan Najeriya durkushewa cikin sauri.<\/p>\n<p>A lokuta da yawa &#8216;yan wasan Najeriya suna buga kwallo ne kawai saboda rashin sana&#8217;a, ko kuma idan wani makwabci ko abokinsu ya tsallaka ya dawo da kudade, kasancewar wasu &#8216;yan kasar suna son yin kudi cikin sauri.<\/p>\n<p>Daga nan, sai suka dauki hanyar a matsayin hanyar samun kudi cikin sauri.<\/p>\n<p>Wannan ya sa da yawa daga cikinsu ba su da kauna da shaukin kwallon, kawai kudin suke bukata.<\/p>\n<p>Da sun buga wa Najeriya burinsu su samu kulob da zai dauke su, ya biya su makudan kudi.<\/p>\n<p>Galibinsu da sun ga wasu kudade makare a asusun ajiyansu, sai su ji kawai sun wuce wajen.<\/p>\n<p>Daga nan, sai su daina dagewa da ci gaba da zage damtsensu.<\/p>\n<p>Hakan yakan cire musu ci gaba da gogayya da takwarorinsu, wanda kuma kwallo idan aka cire gasar, ita kanta ta mutu.<\/p>\n<p><strong>2. <\/strong><strong>Zargin m<\/strong><strong>agudi<\/strong><strong>n shekaru<\/strong><\/p>\n<p>Akwai zargin da aka dade ana yi wato batun cewa yawancin &#8216;yan wasan Najeriya suna zuwa gasar &#8216;yan kasa da shekara 17 a lokacin da shekarunsu ya wuce hakan.<\/p>\n<p>Sai dai wasu suna ganin ba wai kawai a Najeriya ake samun irin wannan matsala ba.<\/p>\n<p>Wasu na ganin, za a iya samun dan shekara 25 daga nahiyar Afirka wanda zai je gasar kasa da shekara 17, don haka bayan shekara biyar, ya zama shekara 30 ke nan a zahiri, amma kuma shekarunsa 22 na kwallo.<\/p>\n<p>Wannan yake sa shakaru su rinjaye shi, kawai sai ka ga kamar an kwashe masa iya kwallon.<\/p>\n<p>Kodayake, hukumomin da ke kula da harkokin kwalloon kafa a kasashen Afirka suna musunta wannan zargi.<\/p>\n<p><strong>3. Siyasa<\/strong><\/p>\n<p>Har ila yau, akwai wadanda suke ganin siyasa ma tana taka muhimmiyar rawa wajen hana &#8216;yan wasa haskawa.<\/p>\n<p>Akwai masu zargin cewa ana samun lokutan da ake sanya son zuciya wajen daukan &#8216;yan wasan, &#8220;inda sai wanda ya san wani ake dauka.&#8221;<\/p>\n<p>Koda kuwa mutum shekarunsa sun wuce, idan yana da uwa a bakin murhu za a iya daukarsa, sai a zubar da wadanda ya kamata a dauka.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hakkin mallakar hoto Getty Images Wannan makala ce da wani mai sharhi kan harkokin wasanni a Najeriya Isiyaku Muhammad Ango ya rubuta mana. A duk lokacin da ake batun &#8216;yan wasan kwallon kafa a duniya, zai yi wuya a shafa fatiha ba tare da an kira Najeriya ba saboda yadda kasar ke fitar da zaratan [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":109220,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[7647,508,11352],"class_list":["post-109219","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","tag-alex-iwobi","tag-bbc","tag-kelechi-iheanacho"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/109219","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=109219"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/109219\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/109220"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=109219"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=109219"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=109219"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}