{"id":106389,"date":"2019-04-12T06:54:02","date_gmt":"2019-04-12T05:54:02","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=106389"},"modified":"2019-04-12T16:32:36","modified_gmt":"2019-04-12T15:32:36","slug":"skwsiy-son-kai-a-zaben-gwamnan-kano-inji-abba-gida-gida","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=106389","title":{"rendered":"Akwai son kai a zaben gwamnan Kano, inji Abba Gida-Gida"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Abba Kabir Yusuf\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2019\/04\/An-yi-son-kai-a-zaben-gwamnan-Kano-\u2014-Abba-Gida-Gida.jpg\" width=\"976\" height=\"549\" data-temp-aztec-id=\"0ad36b9b-5ec8-4893-9904-9801b9b5a9e8\"><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">A ranar Alhamis ne da yamma dai dan takarar jam&#8217;iyyar PDP a zaben gwamnan da aka gudanar a jahar Kanon Najeriya Abba Kabir Yusuf, ya shigar da kara a gaban kotun kararrakin zabe da ke zaman ta a titin Miller a cikin babban birnin jahar.<\/p>\n<p>Abba Kabir Yusuf, ya shaida wa BBC cewa, sun je kotun ne domin su gabatar da dukkan takardunsu na korafe-korafe da lauyoyinsu suka tsara a kan zabukan da suka gudana na gwamna.<\/p>\n<p>Dan takarar gwamnan ya ce, a zaben da aka yi a ranar 9 ga watan Maris, hukumar zabe ta kasa a jihar ta sanar da sakamakon inda ta bayyana cewa jam&#8217;iyyar PDP ce ke kan gaba.<\/p>\n<p>To amma daga bisani hukumar ta ce zaben bai kammala ba, inda aka sake yin wani a ranar 23 ga watan na Maris aka kuma bayyana dan takarar jam&#8217;iyyar APC, wato gwamna Ganduje a matsayin wanda ya samu nasara, bayan kuma kowa ya san duk abubuwan da suka faru a yayin zaben, in ji Abban.<\/p>\n<p>Abba Kabir Yusuf, ya ce su a wajensu sam ba su yarda da sakamakon zaben da aka yi na biyu ba.<\/p>\n<p>Ya ce, sun dauki matakin kin amincewa da sakamakon zaben ne saboda zabe ne wanda kowa a Najeriya ba ma a Kano kadai ba har da ma wasu kasashen duniya suka yi alla-wadai da shi.<\/p>\n<p>Dan takarar gwamnan a jam&#8217;iyyar ta PDP a Kano, ya ce: &#8220;An yi zabe ne na son-kai, an hada baki da jami&#8217;an tsaro, kana an hada baki da su kansu jami&#8217;an hukumar zabe, an sassari wasu, an ji musu ciwo, sannan an ci mutuncin mutane.&#8217;<\/p>\n<p>Ya ce baya ga wadannan abubuwa da aka yi, hatta wakilan jam&#8217;iyyu an kore su daga rumfunan zabe.<\/p>\n<p>Abba Kabir Yusuf, ya ce cin mutuncin ma har &#8216;yan jarida ya shafa.<\/p>\n<figure class=\"media-landscape no-caption body-width\">\n<\/figure>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Karin bayani<\/h2>\n<p>Gwamna Ganduje dai ya kayar da Abba Kabir Yusuf dan takarar babbar jam&#8217;iyyar hamayya ta PDP, bayan sanar da sakamakon zaben jihar da aka kammala a ranar Asabar 23 ga watan Maris.<\/p>\n<p>Ganduje ya ci zaben ne na biyu da tazarar kuri&#8217;a 35,637 inda jam&#8217;iyyarsa ta APC ta samu kuri&#8217;a 45,876 yayin da PDP ta samu 10,239.<\/p>\n<p>Idan aka hada sakamakon zaben na farko da na biyu, jimilla APC ta samu kuri&#8217;a 1,033,695, yayin da PDP ta samu jimilla 1,024,713. Hakan na nufin Ganduje ya ci zaben ne da tazarar kuri&#8217;a 8,982.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>A ranar Alhamis ne da yamma dai dan takarar jam&#8217;iyyar PDP a zaben gwamnan da aka gudanar a jahar Kanon Najeriya Abba Kabir Yusuf, ya shigar da kara a gaban kotun kararrakin zabe da ke zaman ta a titin Miller a cikin babban birnin jahar. Abba Kabir Yusuf, ya shaida wa BBC cewa, sun je [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":106390,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681,4],"tags":[11049,3446,48],"class_list":["post-106389","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","category-politics","tag-abba-kabir","tag-ganduje","tag-inec"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/106389","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=106389"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/106389\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/106390"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=106389"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=106389"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=106389"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}