Ina gaskiyar batun dauke CP Wakili daga Kano?

Tun bayan da aka gudanar da zaben gwamnoni a jihohi 29 a Najeriya, jama’a da dama na ce-ce-ku-ce musamman a shafukan sada zumunta a kan cewa rundunar ‘yan sandan kasar ta dauke kwamishinan ‘yan sandan Kano Mohammed Wakili ta kai shi wata jihar domin ci gaba da aiki.

Mai magana da yawun ‘yan sandan reshen jihar Kano DSP Abdullahi Haruna ya shaida wa BBC cewa wannan labarin da ake yada wa ba gaskiya ba ne.

Jama’a da dama a shafukan sada zumunta sun ta mayar da martani kan wannan lamarin tun bayan da aka fara yada wannan jita-jitar.

Wadannan wasu ne daga cikin zantuttukan da ake yi a shafin Twitter kan batun dauke Wakili daga Kano.

Jama’a da dama a Najeriya sun jinjinawa Mohammed Wakili kan irin tsayuwar daka da ya yi a lokacin zaben gwamna da ‘yan majalisar jihar Kano da aka gudanar a ranar Asabar.

Shi ma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na ll ya jinjinawa kwamaishinan kan irin zage damtsen da ya yi wajen kare dukiyoyi da rayukan jihar Kano.

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Jama’a su kwantar da hankali – Sarkin Kano

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...