Hukumar INEC Ta Dage Zaben Najeriya

Hukumar Zaben Najeriya INEC, ta dage zaben shugaban kasar da za a yi a yau Asabar zuwa 23 ga watan Fabrairu.

A wani taron manema labarai da hukumar ta gudanar dazun nan da misalin karfe 2 na dare agogon Najeriya, Shugaban hukumar Prof. Yakubu Mahmood, ya ce bayan lura da wasu batutuwa da suka shafi shirye-shiryen zaben, hukumar ta lura da cewa, gudanar da zaben ba zai yiwu ba.

“Wannan mataki da hukumar ta dauka bai zo mata da dadi ba, amma ya zama dole a dauke shi, domin zai taimaka wajen samar da sahihin zabe.” Inji Prof. Mahmood.

Ya kara da cewa, “hukumar za ta zauna da masu ruwa da tsaki domin ta fada masu halin da ake ciki a yau da misalin karfe 2 na rana (agogon Najeriya).”

A da, an tsara za a yi zaben na Najeriya a yau Asabar bayan da aka kammala yakin neman zabe a ranar Alhamis.

[

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...