Hukuma ta sake kama rikakken mai satar mutanen nan

Yanzu haka masana da kwararru a Najeriya sun yaba wa ‘yan sanda a kan namijin kokari da suka yi wurin zakulo mutumin, suna cewa wannan na nuna lalle fa ‘yan sandan Najeriya jajirtatttu ne.

Masanin Halayyar bil’adama da harkar tsaro, Farfesa Mohammed Tukur Baba ya ce wannan na nuna irin sabon babi da ‘yan sandan suka bude a sha’anin tsaro, duba da irin bajintar da suke ta nunawa da ba ayi tsammani ba, a don haka matsalolin tsaron da kasar ke fuskanta ba wai ya gagari ‘yan sanda ba ne.

Farfesa Baba ya kara da cewa matakai da suke bi su kamo irin wadannan manyan yan ta’adda ya nuna cewa in sun dukufa kuma suka samu goyon bayan jama’a to fa lalle ‘yan sandan zasu magance matsalolin tsaro a Najeriya.

Kamo irin wannan babban dan ta’addan inji masanin ka iya aikewa da sako ga duk masu son tafka aika aika, don hakan ya fara bada tsoro cewa lalle komai nisan jifa kasa zai fado, don kuwa dan sandan Najeriya ba kanwan lasa bane.

Lauyan nan mai fafutuka Barrister Yakubu Sale Bawa yace shi tuni yana da kwarin gwiwar lalle ‘yan sandan zasu sake cafke shi Wadumen, duba da cewar lalle ‘yan sandan Najeriya in zasu yi aiki zasu yi, kuma cafke wannan Wadumen zai fito da dalla dallan me ya faru.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...