Jam’iyar ta gudanar da taron gangamin yakin neman zabe na dantakarar sanata a zaben cike gurbi da za a gudanar ranar Asabar.
Zaɓen zai gudana ne biyo bayan rasuwar sanata mai wakiltar mazabar, sanata Mustapha Bukar.
Taron gangamin na jam’iyar PDP ya gudana a garin Kankia inda ya samu halartar jiga-jigan jam’iyar PDP da suka fito daga jihohin kasarnan daban-daban.
Cikin jiga-jigan sa suka halarta akwai sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, toshon gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema da sauran mutane da dama.