Hotunan bikin ranar demokradiyya a Najeriya

Najeriya ta yi bikin ranar Demokradiyya ran 12 ga Yuni, don tunawa da sahihin zabe na farko da aka fara yi a kasar ran 12 ga watan Yunin 1993, shekaru goma bayan mulkin soja.

Ga wasu daga cikin hotunan abubuwan da suka faru a lokacin bikin.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Shugaba Muhammadu Buhari da matarsa Aisha Buhari da Mataimakin Shugaban Farfesa Yemi Osinbajo da matarsa Dolapo Osinbajo da sabon Shugaban majalisar dattawa Sanata Ahmad Lawan da sauran manyan baki a wajen bikin.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Daya daga cikin masu nishadantar da mutane a lokacin da take taka rawa a Dandalin Eagle Square da ke birnin Abuja.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, a lokacin da ake tuka shi a mota inda ya ke duban masu faretin girmamawa a Dandalin Eagle Square.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci taron bikin ranar demokradiyyar har da ‘yan kasashen waje.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Faretin ‘yan sanda a lokacin bikin ranar demokradiyya a Abuja, babban birnin Najeriya.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari yana gaisawa da shugaban Rwanda Paul Kagame a lokacin bikin. Daga bayansu kuma tsohon shugaban majalisar dattawan Najeriya ne Ken Nnamani da wasu manyan baki.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wasu sojoji suna fareti a gaban Shugaba Muhammadu Buhari yayin da shi kuma yake kallonsu a Dandalin Eagle Square a lokacin bikin.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Wasu ‘yan rawa suna nishadantar da ‘yan kallo a filin da aka gudanar da bikin a Abuja.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Shugaba Muhammadu Buhari a lokacin da yake jawabi a Dandalin Eagle Square.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Mohammed Abubakar adamu yana sara wa Shugaba Muhammadu Buhari.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...