[HOTUNA]: Zanga-zanga kan Zamfara a Najeriya

'Yan zanga-zanga

Image caption

Wasu daga cikin masu gudanar da zanga-zangar a Abuja babban birnin Najeriya

Jama’a a sassa daban-daban a fadin Najeriya na gudanar da zanga-zanga don nuna bakin cikinsu da yawan kashe-kashen da ake fama da shi a Jihar Zamfara.

Masu zanga-zangar sun hada da mata da maza da tsofaffi da kananan yara da matasa, ‘yan asalin jihar Zamfara da ma wadanda ba ‘yan jihar ba, da suke nuna damuwa da takaicinsu game da abubuwan da suke faruwa.

Image caption

Masu zanga-zangar sun hada da mata da maza

Ana gudanar da zanga-zangar ne a Abuja babban birnin Najeriya da ma sauran jihohin kasar.

Sun yi tattaki daga Unity Fountain zuwa ginin majalisar tarayya.

Image caption

Masu zanga-zangar sun fara ne daga Unity Fountain zuwa fadar shugaban kasa

Masu zanga-zangar sun bayyana cewa, sun gaji da halin ko-in-kula da hukumomi suke nunawa a kan rashin tsaro a jihar.

Image caption

Suna kira ga shugaban kasa da hukumomin tsaro da su dauki matakan gaggawa

“Muna kira ga hukumomin tsaron Najeriya, da mai girma shugaban kasa da a dauki matakin gaggawa game da kashe rayuka a Zamfara, ko sai an gama kashe kowa a jihar sannan za a dauki mataki?”, a cewar daya daga cikin masu zanga-zangar.

Image caption

Suna neman gwamnati ta dauki matakan tsaro don kawo karshen kashe-kashen

Gwamman mutane sun mutu a ‘yan makonni da suka gabata sakamakon hara-haren da aka kai wasu kauyuka a jihar ta Zamfara.

A tsawon shekarun da suka gabata ana ci gaba da samun matsalolin satar mutane don kudin fansa da kuma fyade a wasu kauyuka na jihar.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...