Hajj 2019: Amsar tambayoyinku kan ayyukan da suka shafi Hajji | BBC Hausa

Hajj 2019

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wannan makala ce da ta amsa tambayoyin da masu sauraro suka aiko kan aikin Hajji. Mun yi bincike tare da jin ta bakin Masana kan muhimman abubuwan da suka shafi ayyukan Hajji.

Aikin Hajji, daya ne daga cikin shikashikan Musulunci biyar, da ake wajabta wa Musulmai masu hali su yi ko da sau daya ne a rayuwarsu.

Ana gudanar da aikin Hajji ne a kwanaki biyar wanda ake farawa daga 8 ga Zul Hajji zuwa 12 ko 13 ga watan.

A duk shekara sama da mutum miliyan biyu da rabi ne ke gudanar da aikin Hajji a Saudiyya, wanda shi ne taro mafi girma a duniya.

Hukumar alhazai ta Najeriya ta ce alhazan kasar sama da dubu arba’in ne suka isa Saudiyya domin ibadar.

Kwamishinan Gudanarwa na hukumar Abdullahi Modibbo Saleh ya shaida wa BBC cewa a bana kimanin ‘yan Najeriya 45,000 ne suka aikin Hajjin 2019 .

BBC Hausa ta yi nazari ta hanyar tattaunawa da Malamin Addini kan muhimman abubuwan da suka shafi aikin Hajji, da kuma Kakakin Hukumar Alhazzai ta Najeriya wadanda kuma suka yi kokarin amsa wasu tambayoyi da kuka aiko mana.

Banbamcin Farillai da wajiban ayyukan Hajji

Dakta Mansur Yalwa, Malamin addinin musulunci ne a Najeriya, wanda kuma cikin masu aikin hajjin na bana, ya ce Farillan aikin hajji guda hudu ne, akwai kuma ayyukan da suka wajaba ga mai niyyar aikin hajjin.

Farillan Hajji su ne wadanda idan ba a yi ba Hajjin mutum ya rushe, wato ma’ana hajjin bai yi ba – wajibi kuma za a yi diyya ta hanyar yanka.

Farillan sun kunshi Niyya da Dawafi da sa’ayi (Safa da Marwa) da kuma Arfa.

Ayyukan da ake kira Wajibai sun kunshi Kwanakin da ake yi a Mina da kwanan Muzdalifa da jifan Shaidan da kuma yin aski.

Mutum sai ya yi yanka idan bai yi daya daga cikinsu ayyuka wajibai ba.

Niyya – Mikati

Niyya kamar yadda Dakta Mansur ya fada tun da farko tana daga cikin Farillan Hajji.

Niyyar Hajji tana da iyaka inda ba a wuce wani wuri na daukar Niyya da ake kira Mikati. An fi son mutum ya zo Mikati ya dauki niyyar Hajji ko Umrah.

Malamin ya ce, Mikati wurare ne da Annabi SAW ya yanka wa al’umma na ko wane sashe na duniya inda za su dauki niyya.

“Hadisin Abdullahi bin Umar ya ruwaito Annabi SAW yana cewa – Wasu za su dauki niyya daga Juhfa da Zul-Hulaifa, wasu daga Yalamlam, wasu kuma daga Qarnul Manazil.”

Duk inda ka fito daga duniya ba zaka wuce daya daga cikinsu ba sai ka tsaya ka dauki niyya.

Duk mutanen da suka fara sauka a Madina, Musamman kamar yawancin Maniyyatan da ke fara zaman Madina, kafin isa Makkah to Mikatin da za su dauki niyyar Umrah da Hajji ana kiransa Zul-Hulaifa.

Mikatin yana nan kan hanyar Madina zuwa Makkah inda aka ware kuma aka tanadi wurin wanka domin maniyyata.

Amma Dokta Mansur ya ce wadanda ba za su samu zuwa Madina ba, wato wadanda aka ajiye a Jeddah, za su dauki niyya kafin su sauka daga jirgi saboda kafin Jeddah sun riga sun wuce mikati.

“Idan mutum ya wuce Mikatin shi bai yi niyya ba to yanka ya hau kansa,” in ji Dakta Mansur.

Ya ce asalin Mikatin mutanen Afirka yana wani wuri ne da ruwa ya mamaye wanda ake wucewa a cikin jirgi kafin sauka birnin Jeddah inda ba za a iya tsayawa ba.

Idan Maniyyaci ya riga ya isa birnin Jeddah to ya riga ya wuce inda mikatin yake.

A takaice ba a son a wuce Mikati ba tare da mutum ya yi Ihrami ba, wato wurin ne ake daukar niyyar Hajji ko Umrah.

Nau’in ayyukan Hajji

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Wasu mahajjata sun dafa dakin Ka’aba, wanda ake kewaya wa sau bakwi yayin dawafi

Hajj Ifradi – Wannan da Hausa ana nufin kadaitawa, wato nau’in aikin Hajji ne da za a yi iri daya da niyya daya.

Mutum zai dauki niyyar zai yi Hajji ne kadai ba zai yi Umrah ba, domin Umrah ba farilla ba ce.

Dokta Mansur ya ce Maniyyaci zai dauko niyyarsa daga Mikati ta aikin hajji kadai.

Idan mutum ya sauka Makkah zai fara dawafin isowa. daga nan sai ya gudanar da sauran ayyukan Hajji. Tun ranar da mutum ya shigo zai ci gaba da ayyukansa har zuwa kammala aikin hajji.

Banbamcinsa da sauran nau’ukan aikin Hajji shi ne babu yanka amma sauran ana yanka.

Hajj Tamattu‘i – Shi ne a fara yin Umrah daga baya a yi aikin Hajji.

Hajj Tumattu, shi ne mafi yawanci wanda aka fi yi saboda saukinsa. Malam ya ce ana yin su ne daban-daban, wato aiki biyu da niyya biyu daban.

Mutum zai dauko haramar yin Umrah daga Mikati ba tare da daura niyyar yin aikin Hajji ba.

Kamar wadanda suka kammala zaman Madina, za su tsaya mikati a Zul-Hulaifa su saka harami.

Umrah kuma ta shafi gudanar da abubuwa uku da suka kunshi daura Niyya da Dawafi da sa’ayi (Safa da Marwa).

Bayan an gama sai mutum ya sa kayansa na gida ya zauna Makkah a masaukinsa ya huta har zuwa ranar 8 ga wata da za a fita a fara aikin Hajji.

A Hajj Tumattu’i, maniyyaci zai samu lada biyu na aikin Umurah da Hajji. Kuma ana yin yanka.

Idan mutum ya gama Umrah zai iya yin duk abin da aka hana shi, har saduwa da iyalinsa idan suna tare, a kwanakin da ke tsakanin Umrah da Hajji.

Hajji Kirani – Shi ne a gudanar da aikin Hajji tare da Umrah. Wato za a yi aiki biyu da niyya daya.

A Hajj Kirani, Malam ya ce maniyyaci zai dauki niyya ne daga Mikati cewa zai yi aikin Umrah da hajji a hade.

Yana isa Makka zai yi dawafin isowa sannan ya ci gaba da zama cikin haraminsa.

Idan aka fito aikin Hajji a ranar 8 ga wata ba sai ya sake daukar niyya ba.

Sai idan ya koma Makkah zai yi Dawafi wanda zai kasance matsayin na Umrah da Hajji, bayan kammala ayyukan Hajji, kamar zaman Minna da jifa.

Zai yi Sa’ayi na Hajji da Umrah kuma zai yi aski sannan zai yi yanka.

Malam ya ce Hajj Kirani, galibi mata ne suka fi yawan yinsa saboda matsalar jinin haila da suke yi.

Ya ce idan mace ta dauki niyyar Hajj Tumattu, sai haila ta zo – tana iya canza niyyar zuwa Kirani sai ta jira zuwa lokacin aikin Hajji.

“Za ta iya yin ayyukan Hajji ba ta da tsarki kamar kwanan Minna da Arfa da muzdalifa da jifa,” in ji Dr Mansur.

Haka kuma ya ce idan ta dawo Makkah za ta yi Dawafi na Umrah da Hajji – “kenan ta koma Kirani maimakon Tumattu’i da ta dauko niyya tun da farko.”

Aikin Hajji

Image caption

Mina nan ne ainihin wajen da alhazai ke tafiya a ranar 8 ga watan Zul Hijjah don gudanar da aikin Hajji inda su kan shafe tsawon kwana hudu zuwa biyar. Waje mai matukar girma da aka kafa tantuna don zaman alhazai.

Image caption

Tantunan Mina

Aikin Hajji baki dayansa wuni biyar ne, kuma ana fara wa ne daga 8 ga watan Dhul Hajji.

Amma Malam ya ce zuwa Mina domin shirin zuwa Arfa a ranar ba wajibi ba ne sunnah ce.

Ranar 9 ga wata ake hawan Arfa, sai dai a Arfa ba za a wuce ranar 9 ga wata ba. A ranar 10 kuma a yi Sallah.

Dukkanin wunin 11 da 12 da 13 ana yinsu ne a zaman Mina.

A filin Arfan ne ma’aiki, Annabi Muhammad (S.A.W) ya yi hudubarsa ta karshe kafin ya bar duniya.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Filin arafah shi ne kololuwar wajen gabatar da ibadah a lokacin aikin Hajji. Wannan shi ne dutsen Rahma dake filin Arfah, amma a yanzu an fadada wajen ta yadda ‘yan wasu kasashen ma su kan zauna ne nesa sosai da dutsen saboda irin cikowar da ake yi.

A tsayuwar Arfa ana yin Sallar Azahar da La’asar duka ra’aka biyu. Ana addu’a da zikiri da ambaton Allah a yayin tsayuwar Arfa.

Sai bayan rana ta fadi a wuce Muzdalifa inda za a yi Magariba da kuma Issha, amma kasaru ra’aka biyu.

A Muzdalifa ake kwana cikin harami bayan tsayuwar Arfa, kuma ba a addu’a da karatun Qur’ani mai tsarki, mutum zai kwanta ne ya yi baccinsa zuwa da safe ya wuce zuwa jifa.

Jifa – Ranar Sallah

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Wajen jifan Shaidan da aka fi sani da jamrah na daga cikin wuraren ibada masu muhimmanci lokacin aikin hajji.

A ranar Sallah ne ake yin jifan Jamrah da ake kira jifar Shedan. Kuma ayyuka kusan biyar ne ake yi masu muhimmaci a wannan ranar.

Jamratul Akabah- Wuraren jifa uku ne, amma a ranar sallah daya kawai ake jifa ta karshe. Duwatsu kanana guda bakwai da ba su wuce girman kwayar gyada ko wake ba ake jifa da su, in ji Dakta Mansur Yalwa

Za a iya tsinta tun daga Muzdalifa ko kuma a hanya. Bayan kammala jifa, akan kalli alkibla a yi addu’a. Daga nan sai a yi yanka da kuma aske gashin kai gaba daya, ko kuma saisaye.

Bayan mutum ya yi jifa ya yi yanka da aski, sai ya isa Makkah ya yi dawafi ya yi Safa da Marwa.

Mahajjaji zai cire harami ya je ya yi wanka ya sa kayansa na Sallah idan Tuma’attu’i yake.

A ranar 10 ga wata za a koma Mina a yi kwanakin Minna a ci gaba da zikiri.

Za a dinga zuwa jifa da rana a kwanakin 11 da 12. Daga kwana na 12 mutum zai iya komawa Makkah ko kuma ya sake kwana zuwa 13 ga wata.

Safa da Marwa

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Wannan shi ne wajen Safa da Marwah inda ake so alhazai su yi sassarfa sau biyu daga Safa zuwa Marwa.

Babu banbamcin yadda ake sa’ayi a aikin Hajji da Umrah, haka ma yadda ake Dawafi.

Ana farawa ne a kan Safa a yi addu’a. Sai a tafi zuwa Marwa a matsayin turmi daya. Za a yi haka har sau bakwai.

Hakan na nufin za a fara a Safa a kare a Marwa.

Dutsen Safa da Marwa

kamar yadda Allah ya fada a Alkur’ani mai girma “Lallai ne Safa da Marwa suna daga wuraren ibadar Allah, to, wanda ya yi aikin Hajji a dakin ko kuwa ya yi Umra, to, babu laifi a kansa ya yi dawafi tsakaninsu. Kuma wanda ya kara yin wani aikin alheri to, lallai ne wadannan su ne shiryayyu.” Surah Bakara aya ta 158.

Dutsen Safa inda daga nan ake fara Sa’ayi yana da nisan kilomita 0.80 daga Dakin Ka’aba. Yayin da Dutsen Marwah yake da nisan mita 100 daga Dakin Ka’abah.

Nisan da ke tsakanin duwatsun biyu kuwa mita 450 ne.

Dawafin ban-kwana

Image caption

Dawafi a dakin ka’aba na daga abubuwan da ake so mai aikin hajji ya yawaita

Bayan kammala kwanakin Mina da kammala Sa’ayi da dawaful Ifada, mutum ya kammala aikin hajjin sa. Babu abinnda ya rage masa sai dawaful wada’i, wato dawafin ban-kwana da dakin Ka’abah.

Ana so aikin karshe da mutum zai yi a Makkah gabanin koma wa kasarsa, shi ne dawafi da nufin ban-kwana.

Amma gabanin dawafin, Dakta Mansur yace ana so mai aikin hajji ya ringa yawaita yin sallah a masallacin harami, wato Ka’abah, sannan lokaci zuwa lokaci, ya ringa yin dawafi a dakin.

Zaman Madina

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Maniyyata na zuwa Madina domin yin sallah a masallacin Manzon Allah da kuma ziyartar kabarinsa SAW

Mafi yawancin Maniyyata kan fara sauka birnin Madina domin Ibada a Masallacin Manzo SAW da kuma ziyarce-ziyarce.

Babbar ibadah da ake yi a Madina ita ce gudanar da sallah a masallacin Annabi SAW.

Manzo SAW ya ce sallah guda daya a cikin masallacinsa a Madina, ta fi falala sama da yin sallah a wani masallaci da lada 1,000 idan dai ba msallacin ka’aba ba ne, wanda sallah a cikinsa take da lada dubu dari sama da sauran masallatai.

Wannan falalar ce mutane suke kwadaituwa da ita, saboda muhimmacin samun sallah a masallacin Annabi wanda ya fi komai muhimmacin a garin Madina.

Ana ziyarce ziyarce a Madina, kamar makwancin Manzo SAW a Masallacinsa da kuma sahabbansa a yi masu sallama.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Dakin da ake binne Manzon Allah SAW da Sahabbansa Sayyidina Abubakar da Umar RA.

Dokta Mansur ya ce, ana ziyartar masallacin Quba, wanda Annabi SAW ya fara aza tubalinsa – Annabi ya ce duk wanda ya yi alwala daga gida ko masauki ya je masallacin Quba ya yi sallah zai samu lada kwatantakwacin wanda ya yi Umrah.

Malamin ya ce, ana ziyartar makabartar Baki’a da ke gefen Masallacin Annabi. Sannan kuma ana ziyartar inda aka binne sahabbai 70 da aka kashe a yakin Uhudu da suka hada da Sayyidina Hamza RA.

Ziyartar Makabatar Baki’a sunnah ce wato makabartar da aka binne Sahabbai sama da 10,000. Ana kuma ziyarartar wuraren tarihi, irin Masallaci mai alkibla biyu.

Image caption

Jama’a suna zama domin jiran yin sallah masallacin Madina

More News

Gwamna Ya Maniyata Aikin Hajji Daga Bauchi Sun Samu Tallafin Dubu 900,000

Gwamnan jihar Bauchi,Bala Muhammad ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar ragin ₦900,000 kan kuɗi aikin da za su...

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...