Hadakar Kungiyoyin Kudancin Najeriya Na Kira Ga Fulani

Hadakar kungiyoyin Yarbawa, yankin Naija Delta, da ta jama’ar tsakiyar Najeriya ta Afenifere, da ta Kudancin kasar sun maida martani.

Kungiyoyin sun maida martani ne game da kiran da wata kungiyar Dattawan Arewacin Najeriya tayi cewa, Fulani makiyaya dake zaune a yankin kudancin kasar su dawo Arewa.

Sanarwar wanda shugabannin kungiyoyin irin su Cif Ayo Adebanjo na afenefere dana Chaneze Ndigbo Cif Nnia Nwodo, da Edwin Clark na Naija Delta, suka rattabawa hannun, sunyi Allah wadai da kiran da kungiyar Dattawan Arewa karkashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi tayi na Fulani su koma yankin Arewa domin rayukan su na cikin hatsari.

Koda yake wakilin Muryar Amurka bai samu jin tabakin shugabannin na Afenefere game da wannan sanarwa ba, sarakunan Yarbawa sunyi kira ga Fuani dake wannan yanki da suyi watsi da kiran na barin yankin, su kuma cigaba da gudanar da kiwon dabbobin su, domin tabbatar da zaman lafiya, kamar yadda daya daga cikin sarakunan yarbawa maimartaba Oba Ahmed Adekunle Oyelude ya shaida.

Domin jin tabakin sauran al’ummar yanki dana Arewa, wasu sun ce cece kuce tsakanin kungiyoyin yankin na Arewacin Najeriya da kuma takwarorinsu na Kudanci ko Yanmancin kasar, ya fito ne bayan wani matakin gwamnatin Muhammadu Buhari tace, zata kafa Rugage a yankunan kasar ciki harda Kudu.

Koda yake daga baya ta soke shirin, gwamnati ta fitar da sanarwar ta hannun kakakin fadar shugaban kasa, Malam Garba Shehu inda tayi kira ga Fulanin dake zaune a kudancin Najeriya da suyi watsi da wannan kira da shugaban kungiyar Dattawan Arewacin kasar, farfesa Ango Abdullahi yayi.

Suma ‘yan jam’iyar APC mai mulki a Legas sunyi tsokaci akan wannan al’amarin, kamar yadda daya daga cikin shugaba Alhaji Ado Dansudu yayi bayani.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...