Gwamnatin Uganda za ta haramta ‘cacar’ wasanni

Caca ta zama sana'a ga matasan kasar da yawa
Image caption

Gwamnatin kasar Uganda ta tabbatar da cewa ba za ta sake bai wa kamfanonin caca lasisi a fadin kasarta ba.

Wannan wani yunkuri ne da kasar ke yi domin hana caca a kasar kamar yadda jaridar Daily Monitor ta ruwaito ministan tattalin arzikin kasar, David Bahati, yana cewa.

“Mun samu umurni ne daga shugaban kasa Yoweri Museveni da mu dakatar da cacar wasanni da kamfanonin caca.

Shugaban kasa ya bawa hukumar dake kula da su wannan umurni,” a cewar Mr Bahati.

Ministan ya bayyana cewa shugaban kasar ya bada wannan umurni ne sabado illar da caca ke haifarwa kanana yara a kasar.

Hakkin mallakar hoto
AFP
Image caption

Shugaban kasa Yoweri Museveni ne ya bada umurnin

Cacar wasannin kwallon kafa babbar sana’a ce a kasar kuma tana ci gaba da habbaka.

Matasa da yawa marassa aikin yi a kasar sun shiga harkar caca ne inda suke fatan gina rayuwarsu, kamar yadda BBC ta ruwaito a 2017.

“Daga yanzu, babu wani sabon kamfanin da za a yi wa rajista. Wadanda aka yi wa rajista ba za a sake ba su lasisi ba idan wa’adin sake lasisi yayi.”

Mr Bahati ya fada wa mutane a cikin cocin Rugarama dake garin Kabale.

Ya kuma bayyana cewa Fastocin coci dake adawa da cacar na iya yin murna a yanzu domin addu’arsu an karbe ta.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...