Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayar da wa’adin watanni uku ga dukan baƙin ƙasa da izinin shigarsu ko zama ya ƙare domin su fice daga ƙasar.
Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ce ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, 2 ga Mayu, 2025, wacce mai magana da yawunta, Akinsola Akinlabi, ya sanya wa hannu.
Sanarwar ta ce: “An bayar da wannan damar ne domin ba wa baƙin da bizarsu ta ƙare damar barin ƙasar cikin kwanciyar hankali kafin ranar 1 ga Agusta, 2025.”
Gwamnatin Najeriya Ta Baiwa Baƙin Da Bizarsu Ta Yi Ƴasdaya Wa’adin Kwanaki 90 Su Bar Ƙasar
