Gobara ta kona gidan jigon Darikar Tijjaniyya, Sheik Mansur Kaduna

Shugaban Majalisar Malamai Na kugiyar Fityanul Islam Ta kasa Reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, Imam Murabbi Cisse Alyarwawy Ya Shiga Jerin Sahun ‘Yan Uwansa Jagororin Tarikar Tijjaniyya Da Suka Jajantawa Dan Uwansu Shahararran Malamin nan Na Tariqar Tijjaniyya Sheikh Mansur Kaduna Bisa Jarrabawar Gobara Da Allah Ya yi masa Jiya Da Daddare Misalin karfe 2:00 Na Dare A Gidansa Dake Unguwar Kabala a jihar Kaduna.

Na kira Wayarsa Yau Misalin karfe 9:00 Na Safe Don In Jajantamasa Bayan Na Sami Labarin Abinda Ya Faru Wacce Ta Sabbaba Masa Asarar Dukiya Da Littattafa Masu Yawan Gaske.

Sai Ya Daga Wayata Yana Mai kelkelewa Da Dariya Yana Mai Cewa “Shehu Murabbi Ka ji Abinda Mai Kaya Ya yi Da Kayansa Ko” Sai Ya Dawo Shine Mai Jaje Maimakon Shi Za A Jajantawa.

Take Wannan Dariya Tasa Yayin Ibtila’i Ta Tunatar Da Ni wani Hadithin Sayyidina Abdullahi Bn Umara R.T.A Wanda Imamun Nawawy Ya Kawo Shi Cikin Littafinsa (Al Azkaru).

Ga Hadithin Kamar Haka “Abdullahi Bn Umara Ya Binne Wani Dansa Sai Ya kelqele Da Dariya Sai Aka Ce masa Shin Za ka yi Dariya Wajen kabari Sai Yace Ina So ne n Tirmuza Hancin Shaidan”

Tabbas Na san Ba Komai Bane Ya Janyo Wa Dan Uwa Sheikh Ibrahim Mansur Imam Kaduna Wannan jarrabawar Illa Kusancin sa Ga Allah Da Cikar Kamalar Ma’rifarsa.

Allah Ka Bashi Ikon Cin Wannan Jarrabawa, Ka Azurta shi Da Ninke Niken Abinda Ya Rasa Albarkar Maulana Rasulullahi Sallallahu Alaihi Wa A’lihi Wasallama. Wama Zalika Allallahi Bi Aziz.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...