Gobara ta kona gidan jigon Darikar Tijjaniyya, Sheik Mansur Kaduna

Shugaban Majalisar Malamai Na kugiyar Fityanul Islam Ta kasa Reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, Imam Murabbi Cisse Alyarwawy Ya Shiga Jerin Sahun ‘Yan Uwansa Jagororin Tarikar Tijjaniyya Da Suka Jajantawa Dan Uwansu Shahararran Malamin nan Na Tariqar Tijjaniyya Sheikh Mansur Kaduna Bisa Jarrabawar Gobara Da Allah Ya yi masa Jiya Da Daddare Misalin karfe 2:00 Na Dare A Gidansa Dake Unguwar Kabala a jihar Kaduna.

Na kira Wayarsa Yau Misalin karfe 9:00 Na Safe Don In Jajantamasa Bayan Na Sami Labarin Abinda Ya Faru Wacce Ta Sabbaba Masa Asarar Dukiya Da Littattafa Masu Yawan Gaske.

Sai Ya Daga Wayata Yana Mai kelkelewa Da Dariya Yana Mai Cewa “Shehu Murabbi Ka ji Abinda Mai Kaya Ya yi Da Kayansa Ko” Sai Ya Dawo Shine Mai Jaje Maimakon Shi Za A Jajantawa.

Take Wannan Dariya Tasa Yayin Ibtila’i Ta Tunatar Da Ni wani Hadithin Sayyidina Abdullahi Bn Umara R.T.A Wanda Imamun Nawawy Ya Kawo Shi Cikin Littafinsa (Al Azkaru).

Ga Hadithin Kamar Haka “Abdullahi Bn Umara Ya Binne Wani Dansa Sai Ya kelqele Da Dariya Sai Aka Ce masa Shin Za ka yi Dariya Wajen kabari Sai Yace Ina So ne n Tirmuza Hancin Shaidan”

Tabbas Na san Ba Komai Bane Ya Janyo Wa Dan Uwa Sheikh Ibrahim Mansur Imam Kaduna Wannan jarrabawar Illa Kusancin sa Ga Allah Da Cikar Kamalar Ma’rifarsa.

Allah Ka Bashi Ikon Cin Wannan Jarrabawa, Ka Azurta shi Da Ninke Niken Abinda Ya Rasa Albarkar Maulana Rasulullahi Sallallahu Alaihi Wa A’lihi Wasallama. Wama Zalika Allallahi Bi Aziz.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...